Dan Ganduje Ya Fara Nema Takarar Majalisar Tarayya a NDC Mai Adawa

Dan Ganduje Ya Fara Nema Takarar Majalisar Tarayya a NDC Mai Adawa

  • Ɗan tsohon shugaban APC na kasa, AbdulAziz Ganduje ya sayi fom domin takarar kujerar majalisar wakilai
  • Rahotanni sun nuna AbdulAziz ya bar tafiyar siyasar gidansu tare da komawa sansanin tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso
  • Masu nazarin siyasa sun ce matakin AbdulAziz zai ƙara zafafa fafatawar siyasa a Kano musamman a mazabar Dawakin Tofa, Tofa da Rimin Gado

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Kano - Dan tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya sayi fom domin takarar kujerar majalisar wakilai.

AbdulAziz Abdullahi Umar Ganduje ya tsaya takara a zaben karkashin jam'iyyar adawa ta NDC mai adawa a Najeriya.

Dan Ganduje ya fara neman takara a NDC
Dan Abdullahi Ganduje da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso. Hoto: Rabi'u Musa Kwankwaso.
Source: Facebook

AbdulAziz yana neman wakiltar mazabar Dawakin Tofa da Tofa tare da Rimin Gado a majalisar wakilai ƙarƙashin sabuwar jam’iyyar NDC, cewar Tribune.

Dangantakarsa da siyasa ta kara fitowa fili bayan ya shiga wata takaddama mai cike da ce-ce-ku-ce da mahaifiyarsa, Farfesa Hafsat Umar Ganduje.

Kara karanta wannan

Yadda aka fi ƙarfin gwamnan Kwara kan tsayar da magajinsa, aka zaɓi kakakin majalisa

Abdula'ziz ya kai kara a kanta ga hukumar EFCC kan zargin karya wata yarjejeniya da kuma cin hanci da rashawa.

Ya na neman kujerar majalisar da dan uwansa, Umar Abdullahi Ganduje, ya tsaya takara a karkashin APC a 2023.

Sai dai ya sha kaye a hannun dan takarar NNPP duk da tasirin siyasar mahaifinsu a matsayinsa na gwamna a lokacin.

Dan Ganduje ya fara takara a NDC

Rahotanni sun bayyana cewa AbdulAziz ya raba hanya da tafiyar siyasar gidansu tare da komawa sansanin siyasar tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.

An ga AbdulAziz a wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta yana bayyana manufarsa ta siyasa ga Kwankwaso yayin wata ganawa ta musamman.

Masu lura da harkokin siyasa suna kallon matakin a matsayin babban sauyi a siyasar Kano saboda doguwar adawar APC da tafiyar Kwankwasiyya a jihar.

Ana sa ran AbdulAziz zai fafata da ɗan takarar APC a zaben da ake ganin zai kasance cikin manyan fafatawar kujerar majalisar wakilai a Kano.

Kara karanta wannan

2027: Kakakin majalisar Kwara ya raba gardama a zaben fitar da dan takarar gwamnan APC

Jam’iyyar NDC da Kwankwaso ya koma bayan ficewarsa daga ADC tana ci gaba da samun karɓuwa tare da jawo sababbin magoya baya a Kano.

Masu nazari sun ce takarar AbdulAziz a ƙarƙashin NDC za ta iya sauya kawance tare da ƙara zafafa fafatawar siyasa a mazabar Dawakin Tofa.

Ƙarin bayani na tafe ....

Haidmin Ganduje ya sauya sheka zuwa ADC

A baya, kun ji cewa hadimin tsohon Shugaban APC Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sanar da cewa ya fice daga jam'iyya mai mulki a Kano.

Salihu Tanko Yakasai ya bayyana dalilan da suka jawi ya sauya sheka, duk da har yanzu ubangdidansa a siyasa, Ganduje na APC.

Dan siyasar, wanda aka fi sani da Dawisu a kafafen sada zumunta ya mika bukata ga dukkanin masu goyon bayansu ta yi watsi da jam'iyyar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.