Dan Ganduje Ya Fara Nema Takarar Majalisar Tarayya a NDC Mai Adawa
- Ɗan tsohon shugaban APC na kasa, AbdulAziz Ganduje ya sayi fom domin takarar kujerar majalisar wakilai
- Rahotanni sun nuna AbdulAziz ya bar tafiyar siyasar gidansu tare da komawa sansanin tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso
- Masu nazarin siyasa sun ce matakin AbdulAziz zai ƙara zafafa fafatawar siyasa a Kano musamman a mazabar Dawakin Tofa, Tofa da Rimin Gado
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Kano - Dan tsohon gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya sayi fom domin takarar kujerar majalisar wakilai.
AbdulAziz Abdullahi Umar Ganduje ya tsaya takara a zaben karkashin jam'iyyar adawa ta NDC mai adawa a Najeriya.

Source: Facebook
AbdulAziz yana neman wakiltar mazabar Dawakin Tofa da Tofa tare da Rimin Gado a majalisar wakilai ƙarƙashin sabuwar jam’iyyar NDC, cewar Tribune.
Dangantakarsa da siyasa ta kara fitowa fili bayan ya shiga wata takaddama mai cike da ce-ce-ku-ce da mahaifiyarsa, Farfesa Hafsat Umar Ganduje.

Kara karanta wannan
Yadda aka fi ƙarfin gwamnan Kwara kan tsayar da magajinsa, aka zaɓi kakakin majalisa
Abdula'ziz ya kai kara a kanta ga hukumar EFCC kan zargin karya wata yarjejeniya da kuma cin hanci da rashawa.
Ya na neman kujerar majalisar da dan uwansa, Umar Abdullahi Ganduje, ya tsaya takara a karkashin APC a 2023.
Sai dai ya sha kaye a hannun dan takarar NNPP duk da tasirin siyasar mahaifinsu a matsayinsa na gwamna a lokacin.
Dan Ganduje ya fara takara a NDC
Rahotanni sun bayyana cewa AbdulAziz ya raba hanya da tafiyar siyasar gidansu tare da komawa sansanin siyasar tsohon gwamnan Kano, Rabiu Musa Kwankwaso.
An ga AbdulAziz a wani bidiyo da ya karade kafafen sada zumunta yana bayyana manufarsa ta siyasa ga Kwankwaso yayin wata ganawa ta musamman.
Masu lura da harkokin siyasa suna kallon matakin a matsayin babban sauyi a siyasar Kano saboda doguwar adawar APC da tafiyar Kwankwasiyya a jihar.
Ana sa ran AbdulAziz zai fafata da ɗan takarar APC a zaben da ake ganin zai kasance cikin manyan fafatawar kujerar majalisar wakilai a Kano.

Kara karanta wannan
2027: Kakakin majalisar Kwara ya raba gardama a zaben fitar da dan takarar gwamnan APC
Jam’iyyar NDC da Kwankwaso ya koma bayan ficewarsa daga ADC tana ci gaba da samun karɓuwa tare da jawo sababbin magoya baya a Kano.
Masu nazari sun ce takarar AbdulAziz a ƙarƙashin NDC za ta iya sauya kawance tare da ƙara zafafa fafatawar siyasa a mazabar Dawakin Tofa.
Ƙarin bayani na tafe ....
Haidmin Ganduje ya sauya sheka zuwa ADC
A baya, kun ji cewa hadimin tsohon Shugaban APC Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya sanar da cewa ya fice daga jam'iyya mai mulki a Kano.
Salihu Tanko Yakasai ya bayyana dalilan da suka jawi ya sauya sheka, duk da har yanzu ubangdidansa a siyasa, Ganduje na APC.
Dan siyasar, wanda aka fi sani da Dawisu a kafafen sada zumunta ya mika bukata ga dukkanin masu goyon bayansu ta yi watsi da jam'iyyar.
Asali: Legit.ng