APC Ta Tabbatar da Dauda Lawal a Matsayin Dan Takarar Gwamnan Zamfara a Zaben 2027

APC Ta Tabbatar da Dauda Lawal a Matsayin Dan Takarar Gwamnan Zamfara a Zaben 2027

  • Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal ya lashe tikitin takarar gwamnan na APC ba tare da hamayya ba domin neman wa'adi na biyu a zaben 2027
  • Mamobi da magoya bayan jam'iyyar APC daga mazabun jihar Zamfara sun tabbatar da Gwamna Lawal a matsayin 'dan takara ta tsarin masalaha
  • Da yake jawabi godiya bayan tabbatar masa da takara, Dauda Lawal ya yi alkawarin ci gaba da ayyukan ci gaba idan jama'ar Zamfara suka sake ba shi dama

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Zamfara, Nigeria - Gwamna Dauda Lawal ya zama ɗan takarar gwamna na jam’iyyar APC domin neman wa'adi na biyu a zaɓen gwamnan jihar Zamfara na shekarar 2027.

Jam'iyyar APC mai mulkin Najeriyata tabbatar da Gwamna Dauda Lawal a matsayin dan takararta na gwamna ba tare da hamayya ba yau Alhamis, 21 ga watan Mayu, 2026.

Kara karanta wannan

Gwamna Dikko Radda ya samu tikitin APC, zai nemi tazarce a zaben gwamnoni na 2027

Dauda Lawal.
Gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal yana jawabi a wurin taro a Gusau Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

APC ta ba Gwamna Lawal takara

Gwamna Lawal ya samu tikitin ne ta hanyar tsarin maslaha da jam’iyyar APC ta amince da shi wajen gudanar da zaɓen fitar da gwani a jihar Zamfara, kamar yadda Channels tv ta rahoto

Magoya baya da mambobin jam’iyyar ta APC sun taru a mazaɓu daban-daban na jihar, inda suka amince baki ɗaya da Gwamna Lawal a matsayin ɗan takarar APC.

Yadda aka tabbatar da takarar Dauda Lawal

Sakamakon haka ne kwamitin zaben fitar da gwani na jam'iyyar APC a Zamfara ya tabbatar wa gwamnan da nasara tare da mika masa tutar jam'iyya mai mulki.

Gwamna Dauda Lawal na cikin gwamnonin jihohin Arewa maso Yamma bakwai da ke wa'adi na farko, wadanda za su nemi zarce wa zuwa wa'adi na biyu a babban zaben 2027 mai zuwa.

Gwamna Lawal ya gode wa jam’iyyar APC

Da yake magana da manema labarai bayan kammala taron, Gwamna Lawal ya gode wa mambobin jam’iyyar APC bisa amincewa da suka nuna masa a karo na biyu.

Kara karanta wannan

Ribas: Mutumin Wike na dab da zama 'dan takarar gwamnan APC bayan Fubara ya janye

Ya yi alƙawarin ci gaba da faɗaɗa ayyukan ci gaba da suka shafi inganta rayuwar al’ummar jihar Zamfara, kamar yadda rahoton jaridar Punch ya nuna.

Dauda Lawal.
Gwamna Dauda Lawal yana ganawa da kwamishinoni a taron Majalisar zartarwa a fadar gwamnati da ke birnin Gusau Hoto: Dauda Lawal
Source: Facebook

Ya kuma bukaci mambobin APC a lungu da sako na jihar au hada kai wuri guda domin nasarar jam'iyya a babban zaben da ke tafe.

Gwamna Dauda Lawal dai na cikin gwamnonin jam'iyyun adawa da suka sauya sheka zuwa jam'iyyar APC bayan nasarar da suka samu a zaben 2023 da ya gabata.

Dikko Radda ya samu tikitin jam'iyyar APC

A wani rahoton, kun ji cewa jam'iyyar APC ta tabbatar da Dikko Umaru Radda a matsayin dan takararta na gwamnan jihar Katsina a babban zaben 2027 da ke tafe.

Da yake gabatar da gwamnan ga magoya bayan APC, shugaban kwamitin zaɓen fitar da gwani, Yakubu Machido, ya bayyana Radda a matsayin ɗan takarar APC ta hanyar maslaha.

Ya ce babu wanda ya fito neman takarar gwamnan Katsina a inuwar APC, don haka aka tabbatar da Malam Dikko Radda ba tare da hamayya ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262