Yan Kwankwasiyya, Obidents Sun Shirya Tara Miliyoyi saboda Takarar Obi, Kwankwaso

Yan Kwankwasiyya, Obidents Sun Shirya Tara Miliyoyi saboda Takarar Obi, Kwankwaso

  • Masoyan tsofaffin ƴan takarar shugaban ƙasa, Peter Obi da Rabiu Kwankwaso sun fara shirin neman mafita game da zaben 227
  • Ƴan Kwankwasiyya da Obidienta suna shirin haɗa kai domin takarar shugaban ƙasa a 2027, suna ganin haɗin gwiwa zai kayar da jam’iyya mai mulki
  • Jagoran Obidient Movement, Yunusa Tanko, ya ce magoya baya za su tara miliyoyi domin sayen fom ɗin takarar haɗaka ta Obi da Kwankwaso

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Masoyan Peter Obi da tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso na shiri kan zaben 2027.

Yan Kwankwasiyya da Obidients sun amince su yi aiki tare domin samar da haɗakar tikitin shugaban ƙasa kafin zaɓen 2027.

Yan Kwankwaso, Obi za su tara masu kudi
Sanata Rabiu Musa Kwankwaso, Peter Obi da alamun jam'iyyar NDC Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso/Mr. Peter Obi.
Source: Twitter

Rahoton Arise TV ya ce mutanen sun bayyana cewa haɗin kai ne kaɗai zai taimaka wajen kayar da jam’iyya mai mulki a Najeriya.

Kara karanta wannan

Ana zargin Tinubu ya sake samun matsala da Shettima, zai iya shafar kujeransa

An bayyana wannan matsaya ne a taron masu neman takara na NDC da aka gudanar a Abuja inda ƙungiyoyin Obidient da Kwankwasiyya suka ce za su tattara kuɗaɗe domin tallafa wa haɗakar takarar.

Sun ce jama’a da dama na son shugabanci mai nagarta da gaskiya.

Jagoran Obidient Movement Worldwide, Dakta Yunusa Tanko, ya ce magoya baya za su tara Naira miliyan 60 domin sayen fom ɗin takarar haɗin gwiwa ga Obi da Kwankwaso.

Ya ce wannan mataki yana nuna yadda talakawa suka fara yarda cewa haɗin kai zai ƙara musu ƙarfin nasara.

Tanko ya bayyana cewa haɗakar ta samo asali ne daga buƙatar jama’a na samun shugabanci nagari da kuma wata madadin gwamnati ta gaskiya.

Ya ce mutane daga yankuna daban-daban suna nuna sha’awar mara wa wannan haɗaka baya domin kawo sauyi a ƙasar.

Da yake jawabi a madadin Obi, tsohon shugaban Inter-Party Advisory Council, Cif Peter Ameh, ya bukaci masu neman takara su rungumi gaskiya, sadaukarwa da shugabanci mai kula da talakawa.

Ya ce Najeriya tana buƙatar shugabanni masu kishin ƙasa maimakon masu son anfani da kansu.

Kara karanta wannan

Rigima ta barke a Kaduna, zaben fitar da gwani ya jefa shugaban APC a matsala

Ameh ya yi gargaɗi kan rikici, sayen ƙuri’u da magudin zaɓe, yana cewa shugabanci na gari yana farawa ne daga gaskiya da amana.

Ya ƙara da cewa duniya da kuma ’yan Najeriya na kallon yadda ’yan siyasa za su gudanar da harkokinsu.

Ya kuma soki sauya sheƙar ’yan siyasa bayan cin zaɓe, yana mai cewa hakan na karya amincewar masu zaɓe tare da raunana dimokuraɗiyya.

A cewarsa, dole ne shugabanni su mutunta alƙawuran da suka yi wa jama’a kafin zaɓe.

Shi ma jagoran Kwankwaso National Network, Moshood Shittu, wanda ya wakilci Kwankwaso, ya ce matsalolin Najeriya sun samo asali ne daga rashin shugabanni masu gaskiya da kishin ƙasa.

Ya ce wata rana jama’a za su haɗa kai su ce sun gaji da halin da ake ciki.

Shittu ya bayyana cewa matsalar Najeriya ba ƙarancin arziki ba ce, illa gazawar shugabanni wajen faɗin gaskiya da fifita muradun ƙasa sama da son rai.

Ya ce juriyar magoya bayan talakawa tana nuna cewa lokaci ya yi da za a samu sauyi.

Sakataren NDC na ƙasa, Ikenna Enekweizu, ya tabbatar wa mambobin jam’iyyar cewa za a gudanar da sahihin zaɓen fidda gwani cikin gaskiya da adalci kafin zaɓen 2027.

Kara karanta wannan

Mabiya Obi sun fadi tsarin da Kwankwaso zai mulki Najeriya a 2031

Ya musanta jita-jitar cewa akwai jerin sunayen ’yan takara da aka riga aka tanada a ɓoye.

Enekweizu ya ce duk wanda ya sayi fom zai samu damar shiga zaɓen fidda gwani ko tsarin maslaha cikin gaskiya.

Ya kuma sanar da cewa mata da matasa masu shekaru tsakanin 18 zuwa 35 za su biya rabin kuɗin fom, yayin da masu nakasa za su biya kashi 25 kacal.

Tsohon jigo a NDC, Buba Galadima, ya ce dokar zaɓe ta takaita jam’iyyu zuwa tsarin zaɓen kai tsaye ko tsarin maslaha.

Ya ce wannan tsari an ƙirƙire shi ne domin jefa jam’iyyun adawa cikin matsaloli da rikice-rikice.

Galadima ya tuna yadda zaɓen fidda gwani na kai tsaye a Kano a shekarar 2011 ya jawo mace-mace, raunuka da kuma cin sa tarar naira miliyan 150 lokacin yana sakataren CPC na ƙasa.

Ya ce tsarin kai tsaye kan jawo rikici da shari’u a kotu.

Ya buƙaci jam’iyyu su rungumi tsarin maslaha bayan tattaunawa mai zurfi domin tabbatar da haɗin kai da kauce wa rikicin cikin gida.

Ya ce hakan ne kawai zai taimaka wajen kare jam’iyyun daga matsalolin shari’a da rabuwar kai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.