Atiku Ya ‘Bankado’ Shirin Gwamnoni game da Tazarcen Tinubu a Zaben 2027
- Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya nuna damuwa game da hadin bakin gwamnoni game da zaben Bola Tinubu
- Atiku ya zargi APC da gwamnoni da karkatar da kudaden jama’a domin shirye-shiryen yakin neman zaben 2027 na Tinubu
- Jam’iyyar ADC ta bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa, tana cewa kudaden FAAC ya kamata su je ayyukan raya kasa ba siyasa ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya zargi jam’iyyar APC da gwamnoninta da hadin baki kan zaben 2027.
Atiku ya yi zargin cewa ana karkatar da kudaden jama’a domin shirye-shiryen yakin neman zaben 2027 na Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Source: Twitter
Atiku ya tabo gwamnoni kan zaben 2027
Rahoton Arise News ya ce Atiku ce ana zargin gwamnati da hadin kai da wasu gwamnoni wajen tura kudaden gwamnati zuwa asusun da ake amfani da su wajen harkokin siyasa.

Kara karanta wannan
Kawancen PDP da APM: Gwamna Makinde zai ayyana shiga takarar shugaban kasa a 2027
Jam’iyyar ADC ta bayyana lamarin a matsayin abin kunya, zalunci da kuma laifi mai tsanani ga al’umma.
ADC ta ce a yayin da talauci da yunwa ke karuwa a Najeriya, gwamnoni na APC suna amfani da kudaden jama’a wajen shirye-shiryen siyasa.
Ta kara da cewa kudaden FAAC da ya kamata su je wajen raya kasa ana karkatar da su zuwa asusun siyasa domin yakin neman zabe.
Ya ce:
"Gwamnatin APC da Shugaba Tinubu ke jagoranta na hada kai da gwamnonin APC wajen karkatar da kudaden jama’a zuwa wasu asusun musamman domin yakin neman zaben Tinubu na 2027."

Source: Twitter
ADC ta zargi Tinubu da gazawa a jagoranci
Jam'iyyar ta ce tituna na lalacewa, asibitoci ba su da kayan aiki, makarantu kuma ba su da isasshen kudi duk da yawan kudaden da ake samu.
Ta bayyana cewa wannan lamari ya nuna gazawar shugabanci, inda ake amfani da gwamnati a matsayin hanyar tara kudi don siyasa.
ADC ta bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa cikin gaggawa domin gano gaskiyar zargin karkatar da kudaden FAAC.
Ta ce ’yan Najeriya na da hakkin sanin yadda ake amfani da kudaden su, tare da gargadin cewa za su tuna da duk abin da ke faruwa a yanzu.
ADC ta bukaci a gudanar da bincike mai zaman kansa cikin gaggawa domin gano gaskiyar zargin karkatar da kudaden FAAC.
Ta ce ’yan Najeriya na da hakkin sanin yadda ake amfani da kudaden su, tare da gargadin cewa za su tuna da duk abin da ke faruwa a yanzu.
Atiku ya kadu bayan mutuwar tsohon dan majalisa
A wani labarin, an ji cewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya nuna bacin ransa kan mutuwar Hon. Abba Anas Adamu a hannun masu garkuwa da mutane.
An sace tsohon dan majalisar ne a babban titin Kaduna zuwa Abuja ranar 3 ga Mayu, 2026, inda ya rasu a ranar 12 ga Mayun 2026 duk da kokarin ceto shi.
Atiku ya bayyana faruwar lamarin a matsayin shaida na gazawar gwamnatin Shugaba Bola Tinubu wajen kare rayukan yan kasar da take mulka.
Asali: Legit.ng
