ADC Ta Dura Kan Peter Obi, Ta 'Gano' Manufarsa game da Siyasar Najeriya
- Jam'iyyar ADC ta caccaki tsohon dan takarar shugaban kasa a zaben shekarar 2023, Peter Obi, ta zarge shi da wata manufa
- Kakakin ADC, Malam Bolaji Abdullahi, ya zargi tsohon gwamnan da rashin sanin manufofin jam’iyyar kafin ficewarsa zuwa NDC
- Bolaji ya ce Obi ya fi mayar da hankali kan samun tikitin takara maimakon fahimtar tsarin manufofi da akidar jam’iyyar ADC
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Sakataren yaɗa labarai na jam’iyyar ADC, Bolaji Abdullahi, ya soki tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa, Peter Obi a Najeriya.
Bolaji Abdullahi ya soki Obi ne kan zargin rashin sha’awar sanin manufofin jam’iyyar inda ya ce bukatun kansa ne kawai a gabansa.

Source: Facebook
Kakakin jam'iyyar ya bayyana haka ne yayin hira da gidan jaridar Arise TV da aka wallafa a YouTube inda ya bayyana cewa Obi bai da burin ceto kasar.
Zaben 2027: ADC ta dura kan Peter Obi
Malam Bolaji Abdullahi ya bayyana cewa Obi bai fahimci matsayar ADC a batutuwa kamar tallafin mai da matsalar tsaro ba.
Ya ce jam’iyyar ta ɗauki watanni tana tsara kundin manufofi domin bayyana yadda za ta tafiyar da mulki idan ta samu dama.
A cewarsa, duk wanda ke son canza Najeriya ta hanyar siyasa ya kamata ya san abin da jam’iyyarsa ta tsaya a kai domin samun sauki game da cin zabe.
Bolaji Abdullahi ya kuma yi zargin cewa wasu ’yan siyasa sun fi sha’awar samun tikitin takara maimakon bin akidar jam’iyya da tsarin dimokuraɗiyya.
Ya bayyana ADC a matsayin jam’iyya mai tsayayyen tsari da manufofi, amma wasu na son amfani da ita kawai wajen cimma burinsu na siyasa.
Kakakin jam’iyyar ya ce duk matsin lambar da gwamnati ta saka wa ADC, jam’iyyar ta ci gaba da jajircewa wajen kare dimokuraɗiyya da muradun jama’a.

Source: Facebook
'Abin da Obi ya taba fada' - ADC
Bolaji Abdullahi ya tuna cewa a baya Obi ya taɓa faɗin cewa idan ’yan adawa suka tsaya da ’yan takara biyu, hakan zai bai wa Bola Ahmed Tinubu nasara a 2027.
Ya ƙara da cewa Peter Obi ya samu gata sosai a ADC har aka ba shi damar zaɓar wanda zai riƙe muhimmin ofishin sakataren shirye-shirye na jam’iyyar.
Bolaji ya ce ficewar Obi da Rabiu Musa Kwankwaso zuwa NDC ba sabon abu ba ne, domin an fara shirinta tun bayan wata ganawa da suka yi a Kano.
ADC ta magantu kan fitar da dan takara
Mun ba ku labarin cewa jam’iyyar ADC ta bayyana cewa za ta zaɓi ɗan takarar shugaban kasa ta hanyar amfani da tsarin maslaha domin zaben badi.
Kakakin ADC na kasa, Bolaji Abdullahi, ya bayyana wannan shirin ne yayin wata tattaunawa da aka yi da shi ranar Litinin, 4 ga watan Mayun 2027.
Bayanan na Bolaji Abdullahi sun fito ne sa’o’i kaɗan bayan ficewar Peter Obi da Rabiu Kwankwaso daga ADC zuwa sabuwar jam’iyyar NDC.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

