2027: Mata 6 da Suka Nuna Sha’awar Neman Takarar Gwamna a Najeriya

2027: Mata 6 da Suka Nuna Sha’awar Neman Takarar Gwamna a Najeriya

Yayin da ake ta shirye-shiryen zaben shekarar 2027, an samu mata da dama a Najeriya da suka nuna sha'awar fitowa takarar gwamna.

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Dukkan matan da aka lissafo sun fito ne a karkashin jam'iyyar APC mai mulkin Najeriya a jihohinsu daban-daban a kasar.

Mata 6 da suka nuna sha'awar takarar gwamna a 2027
Sa'adatu Sa'ad Mustapha, Aisha Ahman-Pategi da Iyabo Obasanjo. Hoto: Alkebbar Kaltungo, Aisha Ahman-Pategi.
Source: Facebook

Rahoton The Guardian ta ruwaito cewa daga cikin matan da suka nuna sha'awar takarar akwai guda biyu daga Kwara da kuma biyu daga Ogun.

Har ila yau, daya daga cikin matan ta fito ne daga jihar Gombe karkashin APC yayin da aka sake samun wata daga jihar Nasarawa.

Legit Hausa ta yi bincike tare da jero matan da suka nuna sha'awar rike kujerar da ta fi kowace girma a jihohinsu.

1. Sa’adatu Sa’ad-Mustapha - Jihar Gombe

Hajiya Sa’adatu Sa’ad-Mustapha ta zama mace tilo da ta fito takarar gwamna a Gombe domin zaɓen 2027, cewar Punch.

Kara karanta wannan

An fara tara kudin saya wa El Rufai fam din takarar shugaban kasa a zaben 2027

Sa’ad-Mustapha, tsohuwar kwamishiniyar muhalli da albarkatun dazuzzuka, ta mika takardar bayyana aniyarta a sakatariyar APC ta jihar.

Daga bisani, Sa'adatu ta bayyana goyon bayanta ga dan takarar da Gwamna Inuwa Yahaya ya fitar watau Jamilu Isyaku Gwamna kamar yadda Isma'ila Uba Misilli ya yada a Facebook.

Sa'adatu ta yi mubaya'a ga dan takarar gwamna da aka fitar a Gombe
Hajiya Sa’adatu Sa’ad-Mustapha da ta nuna sha'awar takarar gwamna a Gombe. Hoto: Alkebbar Kaltungo Gombe.
Source: Facebook

2. Fatima Abdulahi - Jihar Nasarawa

Yar siyasa a jihar Nasarawa, Fatima Abdullahi ta nuna sha'awar tsayawa takara domin a fafata da ita a zaben gwamna a 2027.

Fatima ta ce bayyana aniyarta na tsayawa takara duk da Gwamna Abdullahi Sule ya nuna wanda ya ke son ya gaje shi watau Sanata Ahmed Wadada.

Rahoton BusinessDay ya ce Fatima ta bayyana cewa tana da yakinin za ta yi nasara saboda al'umma ne za su yanke hukunci.

3. Aisha Ahman-Pategi - Jihar Kwara

Tsohuwar kwamishiniyar kananan hukumomi da harkokin masarautu a Kwara, Aisha Ahman-Pategi, ta zama mace ta farko da ta bayyana aniyar tsayawa takarar gwamnan jihar a zaɓen 2027.

Aisha Ahman-Pategi, wadda aka fi sani da “Mama Oyoyo”, ta shiga takarar kujerar gwamnan jihar a hukumance, cewar Leadertship.

Kara karanta wannan

APC ta tara N4.4bn daga sayar da fam na takarar 2027 duk da rikicin jam'iyya

Da take jawabi ga dumbin magoya bayanta, Ahman-Pategi ta ce bayyana aniyarta ya zo ne a lokacin da jarumtaka ta haɗu da manufa.

Hajiya Aisha ta fito neman takara a Kwara
Daya daga cikin wadanda suka nuna sha'awar neman takarar gwamna a Kwara, Aisha Ahman-Pategi. Hoto: Aisha Ahman-Pategi.
Source: Facebook

4. Musliat Yetunde Bello - Jihar Kwara

Hajiya Musliat Yetunde Bello, ta ayyana neman takarar gwamna a karkashin jam’iyyar APC a Kwara a zaɓen 2027.

Yetunde ta ce tana da burin dorawa kan nasarorin da Gwamna AbdulRahman AbdulRazaq ya samu, tare da ƙarfafa shigar mata cikin shugabanci, cewar Vanguard.

Da take magana da manema labarai a Ilorin, ta bayyana cewa burinta na takara ya samo asali ne daga hidimar jama’a da kuma ƙoƙarin ƙara yawan mata masu shiga harkokin shugabanci da bunƙasa tattalin arziki.

5. Iyabo Obasanjo - Jihar Ogun

Sanata Iyabo Obasanjo ta koma APC tare da bayyana aniyarta ta tsayawa takarar gwamna a zaɓen shekarar 2027 da ke tafe.

Tsohuwar sanatar ta ce matsin lambar magoya baya ne ya sa ta dawo siyasa bayan kusan shekaru 15 da watsar da ita.

Iyabo ta jaddada cewa APC ce 'gidanta na gaskiya', ta kuma yi watsi da komawa PDP ko ADC masu adawa a Najeriya.

Kara karanta wannan

Da sake: Amnesty ta nemi a bi jinin matasan Kano da aka kashe bayan naɗa Garo

Daga bisani, an yi zama a jihar domin samun damar tsayar da dan takara inda aka amince a ba Sanata Solomon Adeola.

Iyabo ta janye neman takarar gwamna bayan zaman sulhu na APC
Mai neman takarar gwamna a Ogun, Iyabo Obasanjo yayin ziyara ga Bola Tinubu. Hoto@aonanuga1956.
Source: Twitter

6. Modele Sarafa-Yusuf - Jihar Ogun

Tsohuwar yar jaridar wasanni, Modele Sarafa-Yusuf, ta bayyana aniyarta ta tsayawa takarar gwamnan Ogun a zaɓen 2027.

Haka na cikin wata budaddiyar wasika da ta wallafa a shafinta na X, inda Sarafa-Yusuf ta sanar da kudirinta na neman kujerar gwamna.

Dattijuwar ta tabbatar da cewa takararta za ta taimaka wajen tabbatar da zaman lafiya da haɗin kai a jam’iyya.

Ta danganta hakan da abin da ya faru a 2022 lokacin da ta amince da shan kaye ba tare da haddasa rikici ko tada husuma a cikin jam’iyya ba.

Gwamna Inuwa ya nuna magajinsa a Gombe

Mun ba ku labarin cewa jam'iyyar APC reshen jihar Gombe ta tsayar da dan takarar gwamnan domin tunkarar zaben shekarar 2027.

APC ta tsayar da Jamilu Gwamna a matsayin dan takararta na maslaha a zaben shekarar 2027 da ake fuskanta.

Hakan na nufin tsohon Ministan sadarwa, Farfesa Ali Pantami, da sauran masu neman takarar gwamna a APC, ba za su samu tikiti ba idan har ba zaben fidda gwani aka yi ba.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.