Shugaba Tinubu Zai Bar Abuja, Zai Shiga Kasashe 3 kafin Ya Dawo Gida Najeriya

Shugaba Tinubu Zai Bar Abuja, Zai Shiga Kasashe 3 kafin Ya Dawo Gida Najeriya

  • Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu zai yi tafiya ta tsawon makonni biyu zuwa kasashen Faransa, Kenya da Rwanda
  • Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa BolaTinubu zai halarci tarurruka kuma zai gana da shugabanni da yan kasuwa
  • Tinubu zai tafi tare da wasu ministoci da manyan jami’an gwamnati, kuma ana sa ran zai dawo Najeriya bayan kammala taron a Rwanda

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria – Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a ranar Asabar domin fara ziyarar kasashe uku da suka hada da Faransa, Kenya da Rwanda.

Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa wannan tafiya da Shugaba Tinubu zai yi zuwa wadannan kasashe za ta dauki tsawon makonni biyu.

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu na daga hannu kafin jirginsa ya tashi daga filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe, Abuja Hoto: @aonanuga1956
Source: Facebook

Tinubu zai fara zuwa kasar Faransa

Mai ba shugaban kasa shawara kan harkokin yada labarai da dabaru, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X yau Juma'a.

Kara karanta wannan

Dalilin da ya sa Kotun Koli ta dage shari'ar rikicin sarautar Kano zuwa bayan zaben 2027

A cewarsa, shugaban kasar zai fara zuwa Faransa kafin daga bisani ya wuce birnin Nairobi na kasar Kenya domin halartar taron Africa-France Summit da zai fara mako mai zuwa.

Taron Africa-France Summit

Taron wanda shugabannin kasashen Faransa, Emmanuel Macron, da Kenya, William Ruto, za su jagoranta, zai mayar da hankali kan harkokin makamashi, bunkasa masana’antun da ke kare muhalli, fasaha da sauyin yanayi.

"Halartar taron da Tinubu zai yi daga ranar 11 zuwa 12 ga Mayu, 2026 zai nuna kudurin Najeriya na karfafa hadin gwiwa da kasashen Afirka da Faransa," in ji sanarwar.

Taron zai hada shugabannin Afirka da na Faransa domin tattauna muhimman batutuwa kamar bunkasar tattalin arziki, kare muhalli, gina ababen more rayuwa, gina matasa da samar da zaman lafiya.

Abin da Tinubu zai yi a kasar Rwanda

Bayan kammala taron a Kenya, Tinubu zai wuce brinin Kigali na kasar Rwanda domin halartar taron Africa CEO Forum da za a gudanar daga ranar 14 zuwa 15 ga Mayu, 2026.

Taron na bana mai taken “Scale or Fail” zai hada manyan shugabannin kamfanoni, masu zuba jari da masana domin tattauna hanyoyin bunkasa tattalin arziki ta hanyar hadin gwiwa da zuba jari tsakanin kasashe.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya nada sabon Ministan lantarki bayan Adelabu ya yi murabus

An shirya taron ne tare da hadin gwiwar Hukumar International Finance Corporation (IFC), inda ake sa ran halartar sama da shugabanni da jami’ai 2,000.

Shugaba Tinubu.
Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu yana ganawa da baki a Aso Rock Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

A dukkan tarurrukan biyu, ana sa ran shugaba Tinubu zai gabatar da jawaban da za su bayyana sauye-sauyen da gwamnatinsa ke aiwatarwa domin jawo hankalin masu zuba jari da bunkasa tattalin arziki.

Haka kuma zai gana da manyan shugabannin kasuwanci na duniya da na Afirka.

Tinubu zai tafi tare da wasu ministoci da manyan jami’an gwamnati, kuma ana sa ran zai dawo Najeriya bayan kammala taron a Rwanda.

Tinubu ya kare matakin ciyo bashi

A wani labarin, kun ji cewa shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da karbar bashi idan bukatar hakan ta taso.

Tinubu ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a Aso Rock yayin ganawa da masu ruwa da tsaki na jihar Plateau karkashin jagorancin Gwamna Caleb Mutfwang.

Shugaban kasar ya ce karbo aron kudi ba aibu ba ne kuma gwamnatinsa za ta ci gaba da karbowa idan akwai bukatar hakan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262