‘A Sa Ido’: Tinubu Ya Ware Masu Kula da Zaben Fitar da Gwanin Kujerun Majalisar Tarayya
- Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ware manyan masu mukamai a gwamnatinsa domin kula da zaben fitar da gwani a cikin APC
- Tinubu ya zabi Femi Gbajabiamila da Ibrahim Masari alhakin sa ido kan zaɓukan fitar da gwani na APC na yar majalisar tarayya
- Sabon tsarin zai haɗa Gbajabiamila da Masari da gwamnoni, shugabannin APC da majalisar tarayya domin tabbatar da sahihin zaɓen
CHECK OUT: How to Start Earning with Copywriting in Just 7 Days – Even if You’re a Complete Beginner
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Rahotanni sun ce wasu manyan ’yan siyasa na matsa wa Bola Tinubu lamba ya faɗaɗa kwamitin kula da zaben fitar da gwani, amma shugaban ya ƙi.
Majiyoyi sun ce Shugaba Bola Tinubu ya ki amincewa da hakan domin kare tsarin dimokuraɗiyyar jam’iyya wurin zabukan fitar da gwanin.

Source: Twitter
Umarnin Tinubu kan zaben fitar da gwanin APC
Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya umarci shugaban ma’aikatansa, Femi Gbajabiamila, da mai ba shi shawara kan harkokin siyasa, Ibrahim Masari, su jagoranci sa ido kan zaɓukan fitar gwani na APC, cewar Vanguard.
Matakin na zuwa ne bayan tattaunawa tsakanin shugaban ƙasa da sanatoci da ’yan majalisar wakilai da suka buƙaci a tabbatar da dimokuraɗiyya cikin jam’iyyar APC.
Sabon tsarin zai bai wa Gbajabiamila da Masari damar aiki tare da gwamnoni, kwamitin gudanarwa na APC da shugabannin majalisar tarayya wajen gudanar da aikin.
Ana sa ran za su yi aiki tare da shugabannin jam’iyya domin tabbatar da cewa zaɓukan fitar da gwani sun kasance cikin lumana da gaskiya a faɗin ƙasa.

Source: Facebook
Bangaren da kwamitin zai karkata a kai
Sai dai an bayyana cewa sabon tsarin ba zai maye gurbin aikin sakatariyar APC ta ƙasa ba wajen shirya da gudanar da zaɓukan fitar da gwani.
Kwamitin zai fi mayar da hankali kan haɗin kan siyasa, lura da bin doka da kuma taimakawa wajen warware rikice-rikicen da ka iya tasowa yayin da wasu sanatoci suka bukaci tikiti kai tsaye.
Sakatariyar APC ta ƙasa ce za ta ci gaba da fitar da sanarwa, tantance ’yan takara, tura kwamitocin zaɓe da kuma tattara sakamakon zaɓuka.
Rahotanni sun nuna cewa wasu manyan ’yan siyasa na son a ƙara wasu mutane cikin tsarin sa idon domin biyan bukatun ɓangarori daban-daban, kamar yadda TheCable ta ce.
Sai dai Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya ƙi amincewa da hakan saboda gudun kada a raunana tsarin gudanar da sahihin zaɓen fitar da gwani a APC.
Tinubu ya yi fatali da 'bukatar' sanatoci
Mun ba ku labarin cewa Shugaba Bola Tinubu ya gana da Shugabannin majalisar dattawa a fadar shugaban kasa da ke babban birnin tarayya na Abuja.
Wasu sanatocin sun nemi a ba su tikitin takara mai tsaye wanda aka ce shugaban bai amince ba kuma ya nace cewa dole a mutunta tsarin jam’iyya.
Ganawar sirri da aka yi a Aso Villa ta mayar da hankali kan batutuwan kasa masu muhimmanci, inda aka ce an dauki matakai masu karfi ba tare da bayyana su ba.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

