Gwamna Sule Ya Fadi Dalilin Nuna Magajinsa da Ya Rikita APC a Siyasar Nasarawa
- Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya bayyana dalilin zaban Sanata Ahmed Aliyu Wadada a matsayin magajinsa
- Abdullahi Sule ya ce ya yi hakan ne bayan tuntuba mai zurfi, yana mai cewa burinsa shi ne samun ɗan takarar da zai fi sauƙin cin zaɓe
- Ya jaddada cewa tsarin rabon mulki ya shafi yankuna, inda ya bayyana shekarun da yankin Keffi da Lafia suka shafe a kan mulki
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Lafia, Nasarawa - Gwamna Abdullahi Sule na jihar Nasarawa ya sake yin magana bayan nuna wanda ya ke son ya gaje shi.
Gwamna Sule ya fito ya bayyana dalilin da ya sa ya ke son Sanata Ahmed Aliyu Wadada ya kasance magajinsa a Nasarawa.

Source: Facebook
Gwamna Sule ya magantu kan magajinsa a Nasarawa
Hakan na cikin wani faifan bidiyo da shafin Gov. Abdullahi Sule Mandate ya wallafa a Facebook wanda ya yadu a kafofin sadarawa.
Gwamna ya ce ya duba cancantar wanda ya zaba ne domin samun saukin cin zabe ba tare da wata matsala ba.
Ya ce:
"Lokacin da na ke tuntuba, na je na nemo wadanda idan muka ba su wannan mulki za su iya rikewa, a zuciya na ce ina son yin adalci.
"Yankin Keffi sun yi shekaru takwas, Lafia sun yi 12 sai mu kuma za mu yi shekaru 8, idan ina son adalci sai in mayar da mulki yankin Keffi."

Source: Facebook
Yadda gwamna ya zabi magaji cikin 'yan takara
Gwamna Sule ya bayyana cewa da yawa daga cikin masu neman takara sun cancanta amma dole ya duba mafi saukin samun nasara a cikinsu.
Ya ce akwai wanda ya kware a siyasa kuma amininsa ne amma duk da haka bai zabe shi ba saboda tabbatar da adalci.
Ya kara da cewa:
"Duk mutanen nan da suka fito gwamna wallahi duk sun cancanta, za su iya zama gwamna muna da injiniya, muna da likita da sauran su, idan aiki na zan bi sai in ba Farfesa Haruna.
"Akwai wadanda don iya siyasa, ya yi kakakin majalisa sau biyu, kuma babban akanta na ne ya san kudi da gwamnatina, kuma amini na ne."
Gwamna Sule ya ce Sanata Wadada ne a tunaninsa zai fi kawo kujerar gwamna cikin sauki ba tare da wahala sosai ba.
"Akwai kani na Wadada, wanda yanzu yana majalisar tarayya, akwai su da dama, amma na ce su je su zauna, su kawo min mutum daya.
"Daga baya, sai suka hada kai, su ka dawo gare ni, su ka ce kai gwamna mun san kana da adalci, ka je duk wanda ka dauka za mu goyi bayansa.
"Daga nan, na yi tuntuba, sai na ga wanda za a fi samun saukin cin zabe shi ne Wadada, sauran ma za su iya ci amma Wadada zai fi samun sauki."
- Gwamna Abdullahi Sule
Gwamnan jihar Nasarawa ya nada sabon sarki
A baya, an ji cewa an nada Alhaji Suleiman Ahmed-Eko a matsayin sabon Osu Ajiri na Udege, Sarki mai daraja ta daya a al’ummar Afo ta jihar Nasarawa.

Kara karanta wannan
Malami ya umarci mabiyansa a Najeriya su ba 'yan bindiga lambar wayarsa idan aka sace su
Gwamnatin jihar Nasarawa ce ta tabbatar da nadin sabon Sarkin a wata sanarwa da ta fitar yau Laraba, 15 ga watan Afrilun 2026.
An haifi Ahmed Eko a ranar 2 ga watan Yuni, 1972, kuma ya kammala karatu a Kwalejin Fasaha ta Tarayya da ke Nasarawa.
Asali: Legit.ng

