2027: Gwamnoni 4 da Ƴan Majalisa da Ake Zargin Suna Harin Kujerar Kashim Shettima

2027: Gwamnoni 4 da Ƴan Majalisa da Ake Zargin Suna Harin Kujerar Kashim Shettima

  • Ana rade-radin cewa APC na kokarin cire Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima daga tikitin 2027, saboda rikice-rikicen siyasa daga jihar sa
  • Gwamnoni hudu daga Arewa da manyan 'yan majalisa biyu suna zawarcin kujerar mataimakin shugaban kasa
  • Wasu sun ce Shettima bai samu cikakken amincewa daga Shugaba Tinubu ba, duk da cewa suna yawan ganawa da juna a Fadar Shugaban Kasa

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

FCT, Abuja - Makomar siyasar mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima na cikin hadari, yayin da wasu alamu daga cikin jam’iyyar APC ke nuna zai rasa tikitin 2027.

Majiyoyi daga fadar shugaban kasa da APC sun shaida cewa ana wasu lissafe-lissafen siyasa da ka iya sa Tinubu sauya mataimaki.

Ana zargin APC na kokarin sauya Shettima
Ana zargin wasu gwamnoni 4 da ƴan majalisa da harin kujerar Kashim Shettima. Hoto: Kashim Shettima, Asiwaju Bola Tinubu.
Asali: Twitter

Ana hasashen sauya Shettima daga mukaminsa

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da wasu gwamnoni hudu daga Arewa da manyan 'yan majalisa biyu ke harin kujerar mataimakin shugaban kasa, cewar rahoton Punch.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A cewar wata majiya, makarkashiyar na da nasaba da sukar gwamnatin Tinubu da Gwamna Babagana Zulum na Borno da Sanata Ali Ndume ke yi a fili.

Majiya ta ce:

“Babban matsalar Shettima ita ce halayen ‘yan siyasar jiharsa, ciki har da gwamna da Ndume, da ke sukar gwamnati a fili.
“Idan gwamna da sanata daga jiharka, musamman wanda ka damka masa mulki na sukar gwamnati, hakan yana haifar da matsala.”

Zargin Wasu sun fara neman kujerar Shettima

Bayan rikicin taron shugabannin APC na Arewa maso Gabas, an gano cewa wasu sun fara shirya kansu don samun kujerar mataimaki.

Wani jigo ya ce:

“Zai iya yiwuwa domin Shettima ba shi da kusanci sosai da Shugaba, ba a ce za a canza shi ba, amma ba a tabbatar ba.

“Amma hakan bai hana wasu shirya kansu ba, don kada ace idan shugaban ya sauya shawara ko kuma ya yanke hukunci daban.”
Ana ta zarge-zarge kan makomar Shettima a gwamnatin Tinubu
An jero wasu gwamnoni da ake zargin suna neman kujerar Shettima. Hoto: Bayo Onanuga.
Asali: Twitter

Gwamnonin da ake zargin na son kujerar Shettima

Wata majiya ta kara da cewa, jiga-jigai biyu na majalisa da gwamnoni hudu suna da hannu, biyu daga Arewa maso Gabas da biyu daga Arewa maso Yamma.

Gwamnonin da ake tunanin za su maye gurbin Shettima sun hada da na Yobe, Mai Mala Buni, gwamnan Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya.

Sai kuma gwamnan jihar Kaduna, Sanata Uba Sani da kuma takwaransa na jihar Katsina, Dikko Umaru Radda.

Shugabannin majalisar tarayya da aka kira sunayensu

Majiyoyi sun kuma ambaci Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abass da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Barau Jibrin, a matsayin masu zawarcin kujera.

“Yawanci gwamnoni ne ke son wannan kujera sun hada da gwamnan Yobe, Gombe, Kaduna da Katsina duk ana zargin suna da muradi.
“Muna kuma ganin alamun cewa Kakakin Majalisa da Barau Jibrin na sha’awar kujera, dukkaninsu na wakiltar bangarori daban-daban na siyasa."

- Cewar wata majiya

Fadar shugaban kasa ta magantu kan kujerar Shettima

Kun ji cewa Fadar Shugaban Ƙasa ta bayyana cewa Bola Ahmed Tinubu ba zai bayyana wanda zai kasance mataimakinsa a 2027 ba a yanzu.

Hadiminsa shugaban kan harkokin yada labarai, Bayo Onanuga, ya ce yin hakan yana cikin tsarin mulki, kuma babu matsala tsakanin Tinubu da Kashim Shettima.

Bayo Onanuga ya ce jita-jitar cewa za a ajiye Sanata Kashim Shettima sun samo asali ne daga zato da maganganu marasa tushe balle makama.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 3 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.