Majalisar Ta Ayyana Kujerun Sanatoci 2 a Matsayin babu Kowa a Kansu, Ta Ce INEC Ta Canza Zabe

Majalisar Ta Ayyana Kujerun Sanatoci 2 a Matsayin babu Kowa a Kansu, Ta Ce INEC Ta Canza Zabe

  • Majalisar Dattawa ta tabbatar da kujerun sanatoci biyu a matsayin waɗanda babu kowa a kansu, ta bukaci INEC ta shirya zaɓukan cike gurbi
  • Mazaɓun da suka rasa wakilai a Majalisar Dattawa sun haɗa da mazaɓar Sanatan Edo ta Tsakiya da mazaɓar Sanatan Anambra ta Kudu
  • A ranar Talata, shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio ya buƙaci INEC ta cike guraben domin al'ummar mazaɓun su samu wakilci

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

FCT Abuja - Majalisar Dattawa ta bukaci Hukumar Zaɓe (INEC) da ta hanzarta gudanar da zaɓen cike gurbi domin maye gurbin kujerun sanatoci biyu da babu kowa.

Majalisar ta aika wannan saƙo ga INEC ne yayin da ta sake tabbatar da kujerun sanatan Edo ta Tsakiya da sanatan Anambra ta Kudu a matsayin babu kowa a kansu.

Majalisar dattawa.
Majalisar Dattawa ta bukaci INEC ta shirya zaben cike gurbi a Edo da Anambra Hoto: Nigerian Senate
Asali: Facebook

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya sanar da hakan a zaman sanatoci na ranar Talata, kamar yadda Punch ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Zargin lalata: Ɗan Majalisar da ya jagoranci dakatar da Sanata Natasha ya shiga matsala

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya bayyana cewa ya na da matuƙar muhimmanci a cike guraben da suka zama babu kowa a majalisar, domin mazabun da abin ya shafa su ci gaba da samun wakilci.

Dalilin da ya sa babu kowa a kujerun sanatoci 2

Kujerar sanatan Edo ta Tsakiya ta zama babu mai rike da ita ne tun a 2024, bayan da Sanata Monday Okpebholo ya lashe zaɓen gwamna a jihar Edo.

An rantsar da shi a matsayin Gwamnan jihar Edo a watan Disamba na 2024, lamarin da ya sa dole sai an maye gurbinsa a majalisa.

Haka nan kuma, kujerar sanatan Anambra ta Kudu ta zama babu kowa a kanta ne tun bayan rasuwar Sanata Ifeanyi Ubah a watan Yuli na 2024.

Rasuwar sanatan ta haifar da gurbi a majalisar dattawan, wanda har kawo yanzu ba a maye gurbinsa ba, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.

Me ya sa INEC ba ta maye guraben ba?

Kara karanta wannan

Akpabio ya kalubalanci hurumin kotu kan koken Sanata Natasha

Tun a watan Janairun 2025, INEC ta bayyana cewa tana jiran umarni a hukumance daga Majalisar Dattawa kafin ta shirya zaɓen cike gurbi na Anambra ta Kudu.

Kwamishinar zaɓe a jihar Anambra, Elizabeth Agu, ce ta sanar da hakan a wani taron tattaunawa da cibiyar IPC ta shirya a birnin Awka, babban birnin jihar.

Ta bayyana cewa hukumar zaɓe ba za ta iya gudanar da zaɓen ba har sai ta samu bukatar hakan a hukumance daga majalisar, domin a tabbatar da komai ya tafi dai-dai.

Majalisa ta aika saƙo ga hukumar INEC

Kasancewar wadannan mazabu biyu ba su da wakilai a majalisar dattawa, hakan na iya rage tasirin wakilcin al’ummar yankunan a harkokin siyasa da doka.

Wannan ne ya sa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya bukaci INEC da ta hanzarta shirya zaɓen cike gurbi domin mazabun su ci gaba da samun wakilci.

Kotu ta zauna kan shari'ar Akpabio da Natasha

Kara karanta wannan

Akpabio: Majalisa ta lissafo manyan zunuban da suka sanya aka dakatar da Natasha

A wani rahoton, kun ji cewa Godswill Akpabio ya ƙalubalanci babbar kotun tarayya mai zama a Abuja da cewa ba ta da hurumin sauraron karar da Sanata Natasha Akpoti ta shigar.

Sanata Natasha ta kai ƙara gaban kotun ne tana ƙalubalantar matakin ladabtarwa da Majalisar Dattawa ta ɗauka a kanta.

Muhammad Malumfashi, babban edita a sashen Hausa na Legit ya duba labarin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262