Dalibai Mata Sun Diro daga Bene da Wasu Miyagu Suka Kai Hari Kwalejin Lafiya a Najeriya

Dalibai Mata Sun Diro daga Bene da Wasu Miyagu Suka Kai Hari Kwalejin Lafiya a Najeriya

  • Wasu miyagu da ake zargin 'yan daba ne sun kai hari dakin kwanan dalibai mata a Kwalejin Kimiyyar Lafiya da Fasaha ta Ngbo, jihar Ebonyi
  • Rahotannni sun nuna cewa dalibai mata tara sun samu raunuka yayin da suke kokarin tserewa daga saman bene
  • Mahukunta sun ce babu wani dalibi da ya bace bayan harin, kuma ana zargin wasu na cikin makarantar sun taimaka wa maharan

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Ebonyi, Nigeria - Akalla dalibai tara ne suka jikkata bayan wasu da ake zargin 'yan daba ne sun kai hari dakin kwanan dalibai mata na Kwalejin Kimiyyar Lafiya da Fasaha, Ngbo da ke karamar hukumar Ohaukwu a jihar Ebonyi.

Shugabar kwalejin, Gimbiya Chetachi Usulor, ta tabbatar da lamarin a wata sanarwa da ta fitar ranar Laraba, inda ta bayyana cewa harin ya faru ne da misalin karfe 1:20 na dare a ranar 9 ga watan Yunin 2026.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun kai mummunan hari wurin da dalibai ke yin jarabawar WAEC a Kogi

Ebonyi.
Taswirar jihar Ebonyi da ke Kudu maso Gabashin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Mahara sun shiga dakunan dalibab kwaleji

A rahoton Channels tv, Gimbiya Chetachi ta ce maharan sun shiga dakin kwanan daliban tare da fara kwace wayoyin hannu, kudi, katunan ATM da sauran kayayyaki masu daraja daga hannun daliban.

Ta ce bayan ta samu labarin abin da ke faruwa, nan take ta tuntubi jami'an tsaro domin neman dauki.

"Na kira layin gaggawa na 'yan sanda, ofishin 'yan sanda na yankin da kuma jami'an tsaron cikin gida. Da mutane suka fara zuwa wurin, sai maharan suka tsere," in ji ta.

Dalibai 9 sun jikkata yayin tserewa

Shugabar kwalejin ta bayyana cewa daliban da suka samu raunuka ba maharan ne suka kai musu hari kai tsaye ba.

Ta ce wasu daga cikin daliban da ke zaune a saman bene sun yi tsalle suka diro ta tagogi saboda tsoro da kokarin boye wayoyinsu daga hannun maharan.

Gimbiya Chetachi ta ce:

Kara karanta wannan

Tsautsayi: Wani bawan Allah ya rasu da bam ya tarwatse a kan titin Zamfara

"Wasu daliban da ke saman bene sun diro ta tagogi saboda tsoro. Raunukan da suka samu sun samo asali ne daga fadowar da suka yi."

Ta kara da cewa an garzaya da daliban asibiti domin yi musu gwaje-gwaje kamar hoton X-ray da sauran binciken lafiya. A cewarta, dalibai tara ne ke karbar magani a halin yanzu.

Allon sanarwa.
Allon sanarwa na kwalejin lafiya ta Ebonyi da wasu dalibai mata a tsaye bayan harin 'yan daba a dakunansu Hoto: Ebonyi Current News
Source: Facebook

Da gaske wasu dalibai sun bace?

Usulor ta karyata rahotannin da ke cewa wasu dalibai sun bace bayan harin, inda ta jaddada cewa an kirga dukkan daliban kuma babu wanda ya bata.

Shugabar kwalejin ta bayyana cewa akwai yiwuwar wasu daga cikin mutanen makarantar sun taimaka wa maharan, kamar yadda Daily Post ta kawo.

Ta ce rahotanni sun nuna cewa wata mace na cikin mutanen da suka kai harin, inda ake zarginta da nuna wa maharan dakunan da za su shiga su yi sata.

'Yan bindiga sun shiga makaranta a Kogi

An ji cewa 'yan bindiga sun kai mummunan hari makarantar sakandaren gwamnati da ke Iluke Bunu a karamar hukumar Kabba-Bunu ta jihar Kogi.

Kara karanta wannan

Sace dalibai: Gwamna ya umarci rufe makarantu bayan samun rahoton DSS

Rahotanni sun nuna cewa yan bindigan sun yi sanadin mutuwar mutum uku, ciki har da Mataimakin Shugaban Makaranta, Malam Gani Anifowose.

Majiyoyi daga yankin sun bayyana cewa manufar maharan ita ce kai hari kan daliban da ke rubuta jarrabawar WAEC a makarantar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262