Nadin Ministoci: Ba Za Mu Goyi Bayan Wanda El-Rufai Ya Bada Sunan Shi ba – Jigon APC
- Nasir El-Rufai ya tsokano rikici a APC da ya bada sunan wanda zai maye gurbinsa a cikin Ministoci
- A matsayinsa na cikakken ‘dan jam’iyya mai-ci, Muhammadu Murtala zai yaki tsohon jagoransa
- ‘Dan siyasar ya na ganin bai dace El-Rufai ya tsaida wanda yake so ba tare da an zauna da ‘yan APC ba
Kaduna - Muhammadu Murtala ya na cikin jagorori a jam’iyyar APC a jihar Kaduna, ya tattauna da ‘yan jarida game da siyasarsu ta cikin gida.
A wata hira da Daily Trust tayi da shi, Muhammadu Murtala ya yi magana game da wanda ake so ya wakilci Kaduna a majalisar ministoci ta FEC.
Ana tunanin bada sunan Jafar Sani Ibrahim da Malam Nasir El-Rufai ya yi, ya jawo sabani tsakanin ‘ya ‘yan jam’iyyar APC na reshen jihar Kaduna.

Kara karanta wannan
Makiyinka Zai Iya Zama Masoyi: El-Rufai Ya Yi Shagube a Twitter Kafin Nadin Ministoci

Asali: Twitter
Sai an zauna da 'yan APC na Kaduna
Shi Muhammadu Murtala ya na ganin idan har akwai rashin jituwa a kan kujerar minista daga Kaduna, tsohon gwamnan ne ya jawo rigimar.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
‘Dan siyasar ya zargi Nasir El-Rufai da daukar mataki shi kadai ba tare da ya tuntubi sauran ‘yan jam’iyya ba a yayin da aka gagara tantance shi.
"El-Rufai bai tuntube mu ba"
Idan har akwai sabani a cikin jam’iyyar, watakila saboda yadda El-Rufai ya tafi ne da kuma matakin da ya dauka shi kadai na zakulo wani.
Ya tuntubi masu ruwa da tsaki na jam’iyya kafin bada sunan wanda zai canje shi a minista?
Shin ya tuntube mu? Ya shigo jam’iyyarmu, amma babu wanda ya tuntube ni. Sannan ba a tuntubi da-dama daga cikinmu (‘ya ‘yan APC) ba.
Bai sha’awa domin ba a amince da shi ba, kuma sai ya jawo wani a madadinsa. Menene bambancinsa da wanda ya bada, duk daya su ke.
- Muhammad Murtala
A tattaunawa da jaridar, ‘dan siyasar ya nuna ba za su yarda Shugaba Bola Tinubu ya amince da wanda Malam El-Rufai ya kai masa sunansa ba.
Girman ka, girman akwatinka
Kafin a yanke shawara, jigon ya ce sai an zauna da su kamar yadda aka yi lokacin kamfe, sai a dauki wanda ya fi ba jam’iyya gudumuwa a zabe.
"Bai dacewa saboda sanayya a bada sunan wani a mukamin da ke bukatar masu ruwa da tsaki. Zan yi yaki da wannan, mu na da cewa a jam’iyya."
- Muhammad Murtala
Rusau a garin Abuja
Ana da labari kamar yadda Nasir El-Rufai ya yi a Abuja, Nyesom Wike zai yi karin kumallo da makiyaya, ‘Yan Acaba da asu gidaje a birnin tarayya.
Minista ya ce kasuwanni sun yi yawa, haka shanu da 'yan acaba. A cewarsa ba za ta yiwu a rika cin karo da shanu da awaki a kan hanyar Aso Rock ba.
Asali: Legit.ng