Zaben 2027: Kwankwaso Ya Musanta Fitowa Takarar Shugaban Kasa a Inuwar ADC
- Jagoran Kwankwasiyya kuma tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya musanta jita-jitar ayyana takarar shugaban kasa
- Kwankwaso ya tabbatar da cewa har yanzu bai yanke shawarar tsayawa takara ko yi wa wani mataimaki a jam'iyyar ADC ba
- Madugu ya kuma yi karin haske kan rashin gab'ninsa a tarukan jam'iyyar ADC na baya-bayan nan, inda ya ce ya sanar da shugabanni
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kano, Nigeria – Tsohon gwamnan jihar Kano, Rabiu Musa Kwankwaso, ya bayyana cewa bai bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar shugaban kasa ba a halin yanazu.
Tsohon dan takarar shugaban kasa na NNPP ya kuma tabbatar da cewa bai goyi bayan kowane dan takara ba, yana mai cewa duk wata jita-jita kan hakan “ba ta da tushe.”

Source: Twitter
The Cable ta ce wannan na zuwa ne bayan rade-radin da suka yadu tun bayan taron jam’iyyun adawa da aka gudanar a Ibadan, jihar Oyo, inda ake danganta shi da yiwuwar hadakar tikiti da tsohon dan takarar LP, Peter Obi.
Jita-jitar ta kara karfi a kwanakin nan, inda magoya bayan ’yan siyasar biyu ke yada fastocin yakin neman zabe a kafafen sada zumunta.
Kwankwaso ayyana neman takara a ADC?
A wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na Facebook a daren jiya Asabar, 2 ga watan Mayu, 2027, Kwankwaso ya yi watsi da rahotannin, yana mai cewa babu wata matsaya ta karshe da aka dauka kan makomarsa ta siyasa.
Kwankwaso ya kara da cewa sabanin abin da ake yadawa, jam’iyyar ADC ba ta yanke shawara kan tikitin shugaban kasa ba ko kumata zabi dan takara ba.
“Ban bayyana aniyar tsayawa takarar shugaban kasa ba, kuma ban goyi bayan kowa ba. Duk wata jita-jita kan hakan ba ta da tushe.”
Ya kuma yi tsokaci kan hukuncin kotun koli da ya mayar da rikicin shugabancin ADC zuwa babbar kotun tarayya, yana mai cewa hakan ya jefa jam’iyyar cikin mawuyacin hali.

Source: Facebook
Dalilin rashin halartar tarukan ADC
Dangane da rashin halartar wasu tarukan jam'iyyar ADC, Kwankwaso ya ce hakan ya faru ne saboda wasu uzurori na kashin kansa kuma ya riga da ya sanar da shugabannin jam’iyyar tun farko.
Ya jaddada cewa duk wani hukunci da zai dauka kan tafiyarsa ta siyasa za a sanar da shi ne ta hanyoyin da suka dace, ba wai ta jita-jita ba.
Kwankwaso na shirin komawa jam'iyyar NDC?
A wani rahoton, kun ji cewa tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na NNPP, Rabiu Musa Kwankwaso ya yi martani kan wasu rahotanni da ke cewa zai koma NDC.
Sai dai Kwankwaso ya ce babu wata matsaya ta ƙarshe da aka cimma kan makomarsa ta siyasa ko ta magoya bayansa zuwa yanzu.
Jagoran yan Kwankwasiyyya ya bayyana cewa matsalar shari'o'i da rikicin gida da ya sa suka bar jam'iyyar NNPP, yanzu ita ADC ta fama da wadannan rigingimu, inda ya ce sun fara laluben mafita.
Asali: Legit.ng

