Dan Sheikh Nuru Khalid da Ya Koma Kiristanci Ya Dawo Musulunci, Ya Yi Bayanai
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
FCT, Abuja - 'D a ga fitaccen malamin addinin Musulunci, Sheikh Nuru Khalid ya dawo cikin addininsa na asali bayan ya koma kiristanci.
Ibrahim Nuru Khalid ya sanar da cewa a yanzu ya dawo cikin addinin musulunci bayan a kwanakin baya ya fice daga cikinsa.

Source: Facebook
Yaron na fitaccen malamin ya bayyana hakan ne a cikin wani faifan bidiyo da yake magana a cikin wanda aka fitar a shafin Facebook, ranar Talata, 15 ga watan Satumban 2026.
Ibrahim Nuru Khalid ya taba barin musulunci
A kwanakin baya dai Ibrahim Nuru Khalid ya bayyana cewa ya koma cikin addinin Kiristanci bayan ya yi bincike-bincike.
Yaron na fitaccen malamin ya bayyana cewa ya yi duba ga littafi mai tsaki na Al-Kur'ani da bible kafin ya dauki matakin komawa addinin kiristanci.

Kara karanta wannan
Babban malami a Najeriya ya zargi wasu mutane da daukar nauyin 'yan bindiga, ya faɗi dalili
Sauya addinin na sa dai ya jawo cece-kuce da gutsiri tsoma duba da irin girman da mahaifinsa yake da shi da sunan da ya yi wajen karantarwar addinin musulunci.
Wasu kuma sun rika mamaki kan yadda da ga fitaccen malamin zai dauki matakin komawa wani addini daban ba musulunci ba.
Ya dawo cikin musulunci
A cikin sabon bidiyon da ya fitar, Ibrahim Nuru Khalid ya bayyana cewa ya dawo cikin addinin musulunci.
Ya tabbatar da cewa a kwanakin baya ya yi bidiyo inda ya sanar da ficewarsa daga cikin addinin musulunci zuwa kiristanci.
"Sunana Ibrahim Nuru Khalid, a kwanakin baya na yi bidiyo na sauya addini zuwa kiristanci, amma yanzu Allah ya taimake ni na dawo musulunci. Ina kuma neman gafarar musulmi da su yafe mini game da zargin hadisin Annabi Muhammad da na yi.. Sannan kuma ina neman afuwar Allah a kai."
"Ina mai ba da hakuri ga al'ummar musulmai game da wannan kaddara da ta same ni, sannan kuma ina neman addu'ar musulmai gabakidaya domin Allah ya taimake ni na tsaya cikin musulunci tun da dama ni musulmi ne na fita daga ciki."
Ibrahim Nuru Khalid ya kuma tabo batun rashin lafiyar da mahaifinsa ya ce yana fama da ita, inda ya ce ya fi kowa cancanta ys yi magana a kansa.
Asali: Legit.ng