Jita jitar Opay da Shahararrun Labaran Bogi da Suka Rika Yawo Makon Jiya a Najeriya
Nigeria - Labaran karya suna nema su zama ruwan dare musamman shafukan sada zumunta ba a Najeriya kadai ba har da kasashen waje.
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada
A cikin ‘yan kwanakin nan, mun ci karo da wasu labarai da yawa wadanda kirkirar su aka yi ko kuma an yi masu wata fahimta can ta dabam.

Source: Getty Images
Dama can kafar Facebook ta yi kaurin suna wajen tattaro labarai marasa inganci. Wannan matsala ta karu sosai tunda aka kirkiro fasahar AI.
Dandalin X da ya fi shahara da Twitter cike yake da labaran karya na kalamai da aka kikira musamman idan aka shiga fagen kwallon kafa.
Labaran karya da suka yi ta yawo
Legit Hausa ta kawo wasu daga cikin manyan labaran bogin da ta ci karo da su:
1. Opay za su je hutu
Kwatsam aka ga mutane daga ciki har da matashin ‘dan siyasar nan, Adamu Garba II suna yada labari a Facebook cewa Opay za su tafi hutu.
Labarin karyar da aka gani ya yi ikirarin daga 1 ga Satumba 2026 kamfanin zai je hutun sai baba-ga-gani kuma mutane su yi sauri su cire kudinsu.
Kamfanin ya yi maza ya karyata zancen a dandalin X da shafin yanar gizo. Tuni an ba shi shawarar ya yi shari’a a kotu da masu yada sharrin.
2. Soke kwamitin yakin zaben APC
Wasu sun fito suna cewa fadar shugaban kasa ta soke kwamitin yakin neman zaben Bola Tinubu/Kashim Shettima da aka fitar a makon jiya.
Jaridar The Cable ta rahoto Felix Morka yana cewa labarin karya ne, yake cewa maganar soke sunayen ‘yan kamfen da aka fitar jita-jita ce.
Sai dai Kakakin na APC ya ce idan akwai bukatar a sabunta jerin, za a yi hakan. Wannan ya yi daidai da abin da jaridar Legit Hausa ta rahoto.
3. Hafsun tsaro ya yi wa Tinubu mubaya’a
Har bidiyo aka kirkira domin nuna cewa Janar Olufemi Oluyede ya tsoma kan shi a siyasa, yana goyon bayan tazarcen Bola Tinubu a 2027.
Da jin bullar bidiyon karyar, Hedikwatar tsaro ta fitar da jawabi domin karyata zancen, ta ce sharri aka yi wa Hafsun tsaro ta hanyar fasahar AI.
Jawabin ya ce jami’an tsaro suna aikinsu bisa ka’ida ba tare da nuna bangarancin siyasa ba, za a samu labarin karyatarwar a jaridar PM News.
4. Buratai ya ce Tinubu zai kunyata Najeriya?
Yanzu haka ana shari’a a Amurka inda wasu suka bukaci a fito da bayanan shari’ar zargin harkar kwayoyi da aka taba yi da Bola Tinubu.
Wasu ma’abota WhatsApp sun rika yawo da wani hoto mai dauke da cewa Janar Tukur Yusuf Buratai ya ce fitar da bayanan zai kunyata Najeriya.
An yi ikirarin tsohon hafsun sojojin kasar ya fadi wannan. Binciken Legit Hausa ya nuna an juya maganar da tsohon jakadan na Benin ya yi.
Leadership ta rahoto Buratai ya ce abin da ya faru shekaru 33 a Amurka ya wuce, kuma tado maganar za ta iya taba martabar kasar da jama'anta.
5. Sanusi II ya yi wa raddi?
Akwai masu yada cewa Sarki Muhammadu Sanusi II ya yi kaca-kaca da Atiku Abubakar saboda ya yi zancen maido tallafin man fetur.
Wani masoyin Bola Tinubu, Mista Abdullah Ayofe ya daura tsohon bidiyon Sarkin Kano a X lokacin yake magana game da zaben 2023.
Sanusi II ya fada wa masu takaran da ta wuce su shirya daukar matakai masu wahala, ba martani yake maida wa ‘dan takaran ADC a 2027 ba.
Badakalar hukumar bogi cikin gwamnati
Rahoto ya zo cewa Gwamnatin Tarayya ta dakatar da wata hukumar bogi, kafin nan tana shirye-shiryen kiran taron da zai kawo wa Najeriya ₦50bn.
Tun a lokacin Shugaba Bola Tinubu ya ba da umarnin gaggauta kamawa da bincikar shugaban wannan hukuma ta karya, George Buchi Nwabueze.
Ita Gwamnatin tarayya ta musanta sanin zaman hukumar ko labarin gudanar da irin wannan harkar da hadin kan Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya,
Asali: Legit.ng


