An Samu Sabani tsakanin Gwamnati da Dan Majalisa kan Yawan Mutanen da Cuta ta Kashe a Kano

An Samu Sabani tsakanin Gwamnati da Dan Majalisa kan Yawan Mutanen da Cuta ta Kashe a Kano

  • Gwamnatin Kano ta musanta rahoton cewa yara 50 sun mutu sakamakon barkewar cutar mashako watau diphtheria a Rano
  • KNCDC ta ce mutum biyu ne suka mutu a Rano a 2026, yayin da jimillar mutanen da suka mutu a yankin daga Yuli 2023 zuwa Agusta 2026 ta kai 29
  • Cibiyar ta ce kashi 94% na masu kamuwa da cutar ba su samu allurar rigakafi ba, yayin da kashi 91% suka je neman magani ne a makare

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Gwamnatin Jihar Kano ta musanta rahotannin cewa yara 50 sun mutu sakamakon barkewar cutar mashako 'diphtheria' a Karamar Hukumar Rano ta jihar.

Rahoton, wanda aka danganta shi da dan majalisar da ke wakiltar mazabar Rano, Ibrahim Muhammad, ya yi zargin cewa cutar ta yi sanadin mutuwar yara 50 a yankin.

Kara karanta wannan

An shiga yanayin tashin hankali da bam ya tashi da mutane a jihar Zamfara

Abba.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf a fadar gwamnatinsa Hoto: Abba Kabir Yusuf
Source: Facebook

Sai dai a rahoton Channels tv, shugaban hukumar Kula da Cututtuka ta Jihar Kano (KNCDC), Muhammad Abbas, a wata sanarwa da ya fitar ranar Juma’a, ya bayyana ikirarin a matsayin wanda ba a tantance ba.

Mutum nawa cutar ta kashe a Kano?

Abbas ya amince cewa barkewar cutar gaskiya ce kuma ta yi sanadin mutuwar wasu mutane, amma ya ce adadin wadanda ake yadawa bai dace da bayanan da suka tattara ba.

Ya ce bayanan da ake da su sun nuna cewa mutum biyu ne suka mutu sakamakon cutar diphtheria a Rano a shekarar 2026, yayin da jimillar mutanen da suka mutu sakamakon cutar tsakanin Yuli 2023 da Agusta 2026 ta kai 29.

A cewarsa, KNCDC ta samu mutane 32 da suka kamu da cutar a Rano, inda aka yi wa marasa lafiya 25 magani a Cibiyar Kula da Cutar Diphtheria da ke Babban Asibitin Rano, yayin da aka yi wa sauran bakwai magani a Kano.

Kara karanta wannan

Trump ya shiga matukar damuwa bayan rasuwar mawakiyar Amurka, Parton

Dalilin kamuwa da cutar mashako

Shugaban KNCDC ya kuma bayyana cewa kashi 94 cikin 100 na wadanda cutar ta kama ba su samu allurar rigakafi ba, yayin da kashi 91 cikin 100 suka je neman magani ne a makare.

Ya nuna damuwa kan jinkirin kai rahoton wadanda ake zargin sun kamu da cutar zuwa cibiyoyin lafiya, yana mai jaddada cewa gano cutar da wuri da fara magani cikin lokaci na da matukar muhimmanci wajen dakile yaduwarta.

Kano.
Taswirar jihar Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Abbas ya kuma soki dan majalisar bisa zargin yin ikirarin da ba a tantance ba ba tare da tuntubar hukumomin da abin ya shafa ba, ciki har da Ma’aikatar Lafiya ta Jihar Kano da KNCDC.

Ya tambayi yadda mutane 50 za su mutu ba tare da an kai rahotonsu ta hanyoyin da ake amfani da su wajen sa ido kan cututtuka a al’umma ba.

Kano ta nemi agajin gwamnatin tarayya

A wani rahoton, kun ji cewa Kano ta nemi Gwamnatin Tarayya ta tallafa mata bayan an samu karin bullar cutar mashako wato 'diphteria' da ya jawo asarar rayuka da dama.

Daraktan Janar na Cibiyar Kula da Cututtuka ta Jihar Kano (KNCDC), Farfesa Muhammad Abbas, ne ya bayyana hakan yayin wani taron manema labarai da ya gudanar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262