ICPC Ta Jero Sunayen Mutane 13 a Gwamnati, Ta Nemi Tinubu Ya Hukunta Su kan Kafa Hukumar Bogi

ICPC Ta Jero Sunayen Mutane 13 a Gwamnati, Ta Nemi Tinubu Ya Hukunta Su kan Kafa Hukumar Bogi

  • Hukumar ICPC ta bukaci a dauki matakin ladabtarwa kan jami’an gwamnati 13 da ake zargi da hannu a badakalar kafa hukumar PFIPC
  • Hukumar ta kuma bukaci a gurfanar da Prince Adeniyi Adeyemi kan zargin jabun takardu da kwaikwayon matsayi
  • Rahoton binciken ya bayyana yadda PFIPC ta samu damar shiga ofisoshin gwamnati da tsarin hada-hadar kudi duk da cewa ba ta da tushe a doka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Hukumar Yaki da Cin Hanci da Sauran Laifuffuka Masu Alaka da Shi ta Najeriya (ICPC) ta ba da shawarar daukar matakin ladabtarwa kan jami’an gwamnati 13.

Hukumar ICPC ta nemi gwamnatin tarayya ta hukunta wadannana jami'ai ne bisa rawar da ake zargin sun taka wajem kafa hukumar bogi ta PFIPC.

Shugaban ICPC.
Shugaban hukumar ICPC, Musa Adamu Aliyu lokacin da ya gabatar da rahoton bincike ga Shugaba Bola Ahmed Tinubu a Aso Rock Hoto: @ICPCNigeria
Source: Twitter

ICPC ta ba da shawarwari kan PFIPC

Kara karanta wannan

Asiri ya tonu: ICPC ta gano sunayen manyan jami'ai 4 da suka taimaka wajen kafa hukumar bogi

Premium Times ta ruwaito cewa hakan na cikin wani rahoton binciken wucin gadi da ICPC ta gudanar kan yadda hukumar, wadda ba a kafa ta bisa doka ba, ta samu damar shiga ofisoshin gwamnati.

Hukumar ta kuma ba da shawarar gurfanar da Adeniyi Adeyemi, mutumin da ya gabatar da kansa a matsayin Darakta-Janar na PFIPC, bisa zargin kirkirar takardu, kwaikwayon matsayi, bayanan karya da kuma gabatar da bayanan yaudara.

A cikin rahoton wucin gadi da ICPC ta gabatar wa shugaban kasa ranar 6 ga Agusta, 2026, ICPC ta ce gwamnatin tarayya ba ta taba nada Adeyemi ba, sannan PFIPC ba a kafa ta karkashin wata doka.

Jami’ai 13 da ICPC ta ambata

ICPC ta ba da shawarar daukar matakin ladabtarwa kan Mimi Abu, Daraktar Sashen Tsara Kungiyoyi da Ci gaban Ma’aikata a Ofishin Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Tarayya.

Sauran sun hada da;

1. Rosemary Achem, mai ba Darakta-Janar na Ofishin Kasafin Kuɗi na Tarayya shawara ta musamman kan harkokin gudanarwa.

2. Patricia Akhigbe, mataimakiyar darakta a Ma’aikatar Kasafin Kuɗi da Tsare-tsaren Ƙasa.

3. Aminu Abdullahi, jami’in jadawali a Sashen Rabon Ofisoshi, Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya;

Kara karanta wannan

Bayan kwace kadarori 48, EFCC na shirin sake dura kan Abubakar Malami

4. Bello Abdullahi, mataimakin darakta mai kula da IPSAS da National Chart of Accounts a Sashen Asusun Haɗaka na Ofishin Akanta-Janar na Tarayya

5. Sanni Olubunmi, daraktan Sashen Bincike da Sa-ido na Ofishin Akanta-Janar na Tarayya (OAGF);

6. Jousha Kadiri Luka, daraktan Sashen Asusun Haɗaka na OAGF.

7. Muazu Balami, mataimakin darakta mai kula da Harkokin Haɗari da Bita a Sashen Bincike da Sa-ido na OAGF;

8. Omameh Florence, mataimakiyar darakta a Sashen Bincike da Sa-ido na OAGF

9. Akinlose Moses, daga Sashen Bincike da Sa-ido na OAGF

10. Ogaba Harry, babban akanta a OAGF

11. Esther Orji Okoli, babbar jami'a a OAGF

12. Ogunbade Habeebat Ajibola, manaja a Sashen Bin Ka’ida da Dokoki na Hukumar Raya Fasahar Sadarwa ta Ƙasa (NITDA).

Adeyemi.
Shugaban hukumar bogi da aka gano a gwamnatin tarayya, Prince Adeniyi Adeyemi Hoto: @Nigerianstories
Source: Facebook

Hukumar ICPC ta kuma ba da shawarar cewa hukumomin da lamarin ya shafa su aiwatar da gyare-gyaren da aka gano a cikin rahoton binciken.

Hukumar ICPC ta wanke Gbajabiamila

Kun ji cewa ICPC ta kammala binciken ta game da zargin Femi Gbajabiamila da nadin Adeniyi Adeyemi a matsayin shugaban wata hukumar bogi.

Hukumar ICPC ta ce ba ta gano wata hujja da ke nuna cewa Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Femi Gbajabiamila, ya san da zaman PFIPC ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262