Yan Sanda Sun Shammaci Ƴan Bindiga Suna Shirin Satar Kaya a Tirela, Sun Kashe 17

Yan Sanda Sun Shammaci Ƴan Bindiga Suna Shirin Satar Kaya a Tirela, Sun Kashe 17

  • Rundunar ’yan sandan Zamfara ta ce ta kashe ’yan bindiga 17 bayan jami’an tsaro sun yi musayar wuta da su a kan babbar hanyar Funtua zuwa Gusau
  • ’Yan bindigar sun kai hari kan motocin kasuwanci biyu, inda suka kashe direbobi da fasinjoji bakwai, suka raunata wasu tara tare da sace fasinjoji takwas
  • Rundunar ta ce jami’an tsaro sun kaddamar da samame kan maboyar ’yan bindigar, yayin da ake ci gaba da kokarin ceto fasinjojin da aka sace

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Gusau, Zamfara - Rundunar ’Yan Sandan Zamfara ta samu gagarumar nasara a wani samame, inda ta ce ta kashe ’yan bindiga 17 dauke da makamai a jihar.

A ranar 25 ga Agusta 2026, da misalin karfe 4:05 na yamma, rundunar ta samu rahoton cewa ’yan bindiga sun tare babbar hanyar Gusau zuwa Funtua.

Kara karanta wannan

Nasara daga Allah: Yan bindiga da yawa sun baƙunci lahira a jihar Sakkwato

Yan sanda sun kashe ƴan bindiga 17
Sufeta-janar na ƴan sanda, Rilwan Disu yana jawabi. Hoto: Nigeria Police Force.
Source: Twitter

’Yan bindigar sun bude wuta kan direbobi da fasinjoji ba tare da nuna bambanci ba, sannan suka tare wasu motocin haya guda biyu, cewar Tribune.

Daya daga cikin motocin, Sharon da ba shi da lambar rajista, Alhaji Halilu Namadi ne ke tukinsa daga Taloka zuwa Gwagwalada, Abuja.

Dayan motar kuma bas ce ta Hukumar Sufuri ta Jihar Sokoto, SSTA, mai lamba LV 94, wadda Sanusi Musa ke tukawa zuwa Kaduna da Abuja.

A lokacin harin, ’yan bindigar sun harbe direban Sharon har lahira, lamarin da ya sa motar ta rasa iko, ta kife ta kuma fita daga hanya.

Haka kuma, ’yan bindigar sun harbe fasinjoji shida, wadanda suka kunshi maza hudu da mata biyu, har suka mutu.

A bas din SSTA kuma, an harbe wani fasinja namiji har lahira, yayin da wasu fasinjoji tara suka samu raunukan harbin bindiga daban-daban.

’Yan bindigar sun kuma yi awon gaba da fasinjoji takwas zuwa wani wuri da ba a bayyana ba.

Kara karanta wannan

An gano adadin mutanen da yan bindiga suka hallaka a harin masallatan Neja

Bayan samun rahoton gaggawa, Kwamandan ’Yan Sandan Tsafe ya tattara jami’an sashen VCRU tare da jagorantar su zuwa wurin da lamarin ya faru.

An kwashe wadanda suka mutu da wadanda suka samu raunuka zuwa Babban Asibitin Tsafe domin kula da wadanda suka jikkata.

An kuma ajiye gawarwakin wadanda suka mutu a dakin ajiye gawarwaki, yayin da ake jiran tantance su da sanar da iyalansu.

Da misalin karfe 6:45 na yamma a wannan rana, kungiyar ’yan bindigar ta sake kai hari a kauyen Magazu da ke karamar hukumar Tsafe.

A yayin harin, wata harsashi da ta bace ta samu Lawali Muazu, mai shekaru 35, mazaunin kauyen Magazu.

An garzaya da shi Babban Asibitin Tsafe, inda yake samun kulawar likitoci sakamakon raunin da ya samu.

A wani samame na gaggawa, jami’an ’yan sanda da sojoji sun bi sawun ’yan bindigar da suka tsere zuwa babbar hanyar Funtua zuwa Gusau.

’Yan bindigar sun yi yunkurin tare wata motar dakon kaya da ke dauke da kayan abinci domin kwace kayanta.

Da suka ga jami’an tsaro suna zuwa, ’yan bindigar sun yi kokarin tserewa, amma jami’an suka bude musu wuta.

Kara karanta wannan

Gwamna ya dauki zafi da yan bindiga suka kai mummunan hari masallaci ana cikin Sallah

Musayar wutar ta kai ga kashe ’yan bindiga 17, yayin da wasu da dama daga cikinsu suka samu raunukan harbin bindiga.

Rundunar VCRU da sojojin da ke Tsafe suna ci gaba da farautar sauran ’yan kungiyar da suka tsere domin kama su.

Haka kuma, jami’an tsaro suna kokarin ceto fasinjojin takwas da ’yan bindigar suka yi garkuwa da su yayin harin.

Rundunar ta ce a halin yanzu, an shawo kan matsalar tsaro a yankunan da lamarin ya shafa, yayin da ake ci gaba da sintiri.

An tura jami’an ’yan sanda, sojoji, Community Protection Guards, mafarauta da ’yan sa-kai domin kare babbar hanyar da sauran wuraren da ke cikin hadari.

Kungiyoyin tsaron sun kuma fara samamen share fage zuwa maboyar ’yan bindiga da hanyoyin da suke amfani da su.

Kwamishinan ’Yan Sandan Zamfara ya umarci jami’an tsaro su kara kaimi wajen aikin ceto domin kubutar da fasinjojin da aka sace.

Ya kuma bukaci jami’an su tabbatar da cewa an kama ’yan bindigar da suka tsere tare da gurfanar da su gaban kuliya.

Kara karanta wannan

An samu karin yan ta'addan ISWAP sama da 20 da suka mika wuya ga sojoji

Rundunar ta bukaci jama’a su kasance cikin taka-tsantsan tare da kai rahoton duk wani motsi ko hali da suke zargi ga ofishin ’yan sanda mafi kusa.

Bam ya kashe mutane a Zamfara

An ji cewa rahotanni sun nuna cewa mutane biyu sun mutu bayan wani abin fashewa da ake zargin bam nd ya tashi a hanyar Gurusu-Gwashi ta jihar Zamfara.

Majiyoyi daga yankin da lamarin da auku sun bayyana cewa ana zargin wani babur ne ya taka bam ɗin da aka binne a ƙasa a Bukuyyum.

Dakarun rundunar sojoji sun ci gaba da sintiri da mamaye yankin domin hana sake kai makamancin wannan hari da kuma bincike wurin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.