An Fara Guna Guni bayan Rashin Sanin inda Shugaban INEC Ya Shiga
- Obidient Movement ta nemi INEC ta bayyana inda Shugabanta, Farfesa Joash Amupitan, yake bayan Rhoda Gumus ta bayyana a matsayin shugabar riƙon kwarya
- Ƙungiyar ta ce babu sanarwar hukuma da ta bayyana lokacin ko dalilin da ya sa Amupitan ya miƙa ragamar hukumar ga Gumus
- Ta kuma nemi INEC ta bayyana ko Amupitan ya fita daga ƙasar da kuma irin ayyukan hukuma da ya gudanar yayin da ba ya hedikwatar hukumar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - Ƙungiyar Obidient Movement ta nemi Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC) ta yi bayani kan inda shugabanta, Farfesa Joash Amupitan, yake da kuma ayyukan da yake gudanarwa.
Ƙungiyar ta yi wannan buƙatar ne bayan Kwamishiniyar INEC ta Ƙasa, Farfesa Rhoda Gumus, ta bayyana a matsayin shugabar riƙon kwarya yayin wani taro da tawagar Tarayyar Afirka (AU) a Abuja.

Source: Facebook
Gumus ta karɓi tawagar AU
A ranar Talata, 15 ga Satumba, INEC ta wallafa wani saƙo a shafinta na X, inda ta bayyana Gumus a matsayin shugabar riƙon kwarya ta hukumar.
Gumus ce ta karɓi Tawagar Bincike da Tantance Buƙatun Zaɓe ta Tarayyar Afirka, wadda ta ziyarci hedikwatar INEC da ke Abuja.
Tawagar, ƙarƙashin jagorancin tsohon Ministan Harkokin Wajen Habasha, Demeke Mekonnen, ta je Najeriya ne domin tantance shirye-shiryen ƙasar na babban zaɓen 2027.
Gumus na cikin kwamishinonin INEC na kasa, kuma sunanta yana cikin jerin kwamishinonin da aka wallafa a shafin hukumar.
Obidient Movement ta nemi bayani
A cikin wata sanarwa da jagoran kungiyar na kasa, Dr Yunusa Tanko, ya sanya wa hannu a shafin X, ƙungiyar ta ce bayyanar Gumus a matsayin shugabar riƙon kwarya ta haifar da tambayoyi kan inda Amupitan yake.
Tanko ya ce, a saninsu, babu wata sanarwa daga INEC da ta bayyana cewa Amupitan ya miƙa aikinsa ga wani mutum, ko a matsayin riƙon kwarya ko na dindindin.
“A wajen Obidient Movement da ’yan Najeriya, babu wata sanarwar da ta bayyana cewa Farfesa Amupitan ya miƙa ragamar aikinsa ga wani, ko a matsayin riƙon kwarya ko na dindindin,” in ji shi.
Ya ce hakan ya haifar da tambayoyi kan inda shugaban hukumar yake a yanzu, jadawalin ayyukansa da kuma dalilin rashin kasancewarsa a hedikwatar INEC.
An nemi INEC ta bayyana tafiyarsa
Ƙungiyar ta nemi INEC ta bayyana inda Amupitan yake, lokacin da ya bar Abuja da kuma dalilin da ya sa ya yi hakan.
Ta kuma nemi hukumar ta bayyana wanda ya ba da izinin tafiyar, da kuma ko shugaban ya fita daga ƙasar.
Idan ya fita daga Najeriya, ƙungiyar ta ce INEC ya kamata ta bayyana irin ayyukan da ya gudanar a wajen ƙasar.
Ta tambayi ko ya gana da Tinubu
Obidient Movement ta kuma nemi INEC ta bayyana ko Amupitan ya gana ko kuma yana da shirin ganawa da Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
Haka kuma, ta nemi bayani kan ko shugaban hukumar ya gana ko yake shirin ganawa da Shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, ko kuma wani wakilin jam’iyyar mai mulki.
Ƙungiyar ta ce irin waɗannan bayanai na da muhimmanci domin a fahimci yanayin ayyukan hukumar da kuma dalilin da ya sa Kwamishina Gumus ke gudanar da ayyukan shugaban INEC a halin yanzu.

Source: Facebook
ADC ta aika sako ga INEC
A wani labarin kuma, kun ji cewa jam’iyyar African Democratic Congress (ADC) ta mika bukatar ta ga Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa (INEC).
Jam'iyyar ADC ta bukaci hukumar INEC ta hana malaman jami’a da aka san suna da alaƙar siyasa zama jami’an tattara da haɗa sakamakon zaɓen 2027.
Asali: Legit.ng


