Ana Wata ga Wata: Gwamnatin Tinubu Za Ta Kara Cire Wani Tallafi a 2027
- Gwamnatin Tarayya karkashin jagorancin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta ce za ta kawo ƙarshen biyan tallafin wutar lantarki a Najeriya daga 2027
- Ministan Wutar Lantarki, Joseph Tegbe, ya ce za a cire tallafin a hankali tare da biyan tsoffin basussukan ɓangaren wutar lantarki
- Ya ce babu shirin ƙara kuɗin wutar lantarki nan take yayin da gwamnati ke shirin kawo ƙarshen tallafin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja - Gwamnatin Tarayya ta sanar da shirin kawo ƙarshen biyan tallafin wutar lantarki a Najeriya daga 2027 domin samar da tsarin da zai dawwama a ɓangaren wutar lantarki.
Ministan Wutar Lantarki, Joseph Tegbe, ya bayyana hakan yayin wata ganawar manema labarai ta baya-bayan nan.

Source: Instagram
Tribune Nigeria ta rahoto cewa ministan ya yi magana kan yawan basussukan da suka dabaibaye ɓangaren wutar lantarki da kuma shirin gwamnati na hana ƙaruwar basussuka.
Yadda aka tsara cire tallafin lantarki
Tegbe ya ce gwamnati za ta cire tallafin a hankali yayin da take aiki wajen biyan tsoffin basussukan ɓangaren.
“Mun samu umarnin Shugaban Ƙasa na biyan tsofaffin basussuka da kuma samar da tsare-tsare masu ɗorewa domin tabbatar da cewa ba a ƙara tara wasu basussuka ba,” in ji Tegbe.
Ministan ya ce shirin cire tallafin ba yana nufin yan Najeriya za su rasa fa’idodin da suke samu a yanzu ba, yana mai tabbatar cewa gwamnati za ta ci gaba da ƙoƙarin inganta samar da wutar lantarki.
“Na yi muku alkawari, shekara mai zuwa, da yardar Allah, za mu kawo ƙarshen wannan abin da ake kira tallafi a ɓangaren wutar lantarki.
"Shugaban Ƙasa ba zai hana Najeriya wani abu ba. Za mu tabbatar da cewa masu amfani da wutar lantarki a Najeriya sun ci gaba da samun wuta tare da inganta ayyukan wutar lantarki,” in ji shi.
Shin za a kara kudin wuta a Najeriya?
Tegbe ya kuma ce babu wani shirin gaggawa na ƙara kuɗin wutar lantarki yayin da gwamnati ke shirin kawo ƙarshen tallafin.
Ministan ya bayyana cewa an samu ci gaba wajen samar da wutar lantarki, inda wasu wuraren da a baya suke fama da dogon lokaci ba tare da wuta ba yanzu suke samun wutar lantarki har na tsawon sa’o’i 18 a rana.

Source: Facebook
“Wuraren da ba su da wuta kwata-kwata tsawon watanni uku yanzu suna samun wuta na tsawon sa’o’i 18. Wasu wurare sun kira ni suka ce, ka rage gudu, komai da ke cikin firijinsu yana daskarewa," in ji shi.
Tegbe ya tuna cewa a lokacin tantance shi da Majalisar Dattawa, ya yi alkawarin cewa ’yan Najeriya za su fara ganin sauyi a samar da wutar lantarki cikin watanni uku zuwa shida.
Ministan Tinubu ya cika baki kan lantarki
Kun ji cewa Joseph Tegbe, ya bayyana cewa yadda mutane ke samun wutar lantarki ba katsewa ya sa wasu ƴan ƙasa roƙonsa ya rage ƙarfin wutar da ake kawowa.
Ministan ya amince da ƙalubalen da ke gaban ɓangaren, inda ya bayyana cewa yawancin kayayyakin lantarki a ƙasar sun wuce shekaru 40.
Asali: Legit.ng

