Sunayen Mutum 20 da ke Jagorantar Sabuwar Hukumar Bogi a Jihohin Najeriya
- Rahotannin da suka fito sun nuna cewa ana zargin wata hukumar bogi da samun tsari mai rassa a jihohi 20 da kuma kasashen China da Amurka
- Shafin yanar gizon hukumar ya bayyana George Buchi Nwabueze a matsayin babban darakta na kasa, tare da daraktoci da masu kula da jihohi
- Hakan na zuwa ne bayan shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar da umarnin kama Nwabueze tare da dakatar da sakatarorin gwamnati kan hukumar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf Kari yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Abuja – Wasu bayanai sun bayyana yadda wata hukumar bogi ta NBDMN ta samar da tsari mai yalwa a jihohi daban-daban na Najeriya da ma kasashen waje.
Rahoto ya nuna nuna cewa shafin yanar gizon hukumar ya lissafo wani mutum mai suna Hon. Nwabueze George a matsayin shugaban hukumar.

Source: Facebook
Punch ta wallafa cewa hukumar na da daraktan gudanarwa na kasa, daraktocin shiyya uku, masu kula da jihohi 20 da kuma wakilai a kasashen Amurka da China.
Shugaban hukumar da ake zargi
Wannan bayani ya zo ne bayan Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC), Musa Aliyu, ya bayyana cewa shugaban kasa Bola Tinubu ya bayar da umarnin gaggauta kama George Buchi Nwabueze.
ICPC ta bayyana Nwabueze a matsayin wanda ya kafa ko kuma yake jagorantar hukumar da ake zargin tana gudanar da ayyuka ba tare da sahalewar shugaban kasa ba.
An kuma gano cewa mutumin yana amfani da sunaye daban-daban, ciki har da George Nathan Nwabueze, George Buchi Nwabueze, Prince George Buchi Nwabueze da kuma George Nwabueze.
An gano masu kula da jihohi 20
Rahoton ya nuna cewa hukumar da ake zargi ta nada masu kula a jihohi 20 na Najeriya, wadanda suka hada da Katsina, Kaduna, Delta, Kebbi, Osun da Anambra.
Sunayen da suke shafin hukumar su ne:
- Dr Babangida Kabir Ruma — Katsina
- Hon. Abdulhaleem Ishaq Ringim — Kaduna
- Hon. Dr Godwin Adolor — Delta
- Hussaini Abdullahi, Esq., FSI — Kebbi
- Hon. Olugbemi Adetola Adelowokan — Osun
- Hon. Chiamaka Nnake — Anambra
- Hon. Osolafia Muhammed, PhD — Nasarawa
- Mrs Salome Audu Bidda — Plateau
- Hon. Orduen Andrew Ikon — Benue
- Amb. Orioye G. Benedict — Ondo
- Hon. Engr. Kehinde Akintonide, FNSE — Ogun
- Hon. Ibrahim Umar Aliyu — Sokoto
- Hon. Mrs Nwosu Chinyere R. — Abia
- Hon. Ibrahim Bello Marafa — Zamfara
- Haj. Zainab Mohammed — Niger
- Hon. Abubakar Ahmad Bichi (Khalifa) — Kano
- Hon. Justin Aondoaseer Tyopuusu — Taraba
- Alhaji Bello Kolawole Ghaffar, FCA — Oyo
- Hon. Farouq Siyi — Bauchi
- Hon. Olorukooba Bidemi — Kogi

Source: Facebook
Tinubu ya ce a dauki mataki
A wani labarin, mun ruwaito cewa Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (ICPC) ta bayyana cewa ta gano wata hukumar bogi da ke aiki a Najeriya.

Kara karanta wannan
Akwai matsala: Ruwan koguna na shirin ɓallewa ya afka cikin Kaduna, Jigawa da wasu jihohi
ICPC ta ce ana zargin George Buchi Nwabueze da kafa ko tallata hukumar tare da zargin hadin gwiwar wasu manyan jami'an gwamnati a Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya.
Shugaban ICPC, Dr Musa Adamu Aliyu, SAN, ya bayyana hakan ne a fadar shugaban kasa da ke Abuja bayan ganawa da shugaban kasa Bola Tinubu.
Asali: Legit.ng

