Jihar Ondo
An shiga wani irin yanayi bayan mutuwar mai neman tikitin gwamnan jihar Ondo a jam'iyyar APC, Dakta Paul Akintelure a yau Talata 26 ga watan Maris a jihar.
Yayin da ake ta shirye-shiryen gudanar da zabe a jihar Ondo, Gwamna Lucky Aiyedatiwa ya sake gamuwa da cikas bayan jigon APC ya gargade shi kan sake tsayawa takara.
Ga dukkan alamu shugaban majalisar dokokin jihar Ondo, Oladiji zai fuskanci barazanar tsigewa bayan ya ari bakin ƴan majalisa ya ci musu albasa ba da yawunsu ba.
Dan takarar gwamnan APC a jihar Ondo, Olusola Oke ya sha alwashiin lashe zaben gwamnan jihar Ondo a bayan rashin nasara kamar Muhammadu Buhari a karo na uku.
Kungiyoyin ma'aikatan Jami'o'i na SSANU da NASU sun shirya shiga yajin aikin gargadi na tsawon kwanaki bakwai kan rashin biyan su albashi na watanni huɗu.
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, ya bayyana dalilin da ya sa tsohon gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu, ya yi nasara kan PDP a zaben gwamnan jihar na 2020.
Betty Akeredolu, Matar tsohon gwamnan Ondo, Rotimi Akeredolu ta caccaki surukarta, Funke Akeredolu Aruna bayan ta nuna goyon baya ga Gwamna Lucky Aiyedatiwa.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi magana kan halin kuncon da aƙe ciki a kasar nan. Shugaban kasan ya ba 'yan Najeriya sabon tabbaci don samo mafita.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya ce abu ne mai matuƙar wahala a iya ciye gurbin da marigayi tsohon gwamnan jihar Ondo, Rotimi Akeredolu ya mutu ya bari.
Jihar Ondo
Samu kari