Ana Wata ga Wata: Shugaban Majalisar Dokoki Ya Yi Murabus bayan Ya Gano Shirin da Aka Masa

Ana Wata ga Wata: Shugaban Majalisar Dokoki Ya Yi Murabus bayan Ya Gano Shirin da Aka Masa

  • Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Edo, Rt. Hon Blessing Agbebaku, ya yi murabus daga mukaminsa a yau Litinin, 17 ga watan Agusta, 2026
  • Rahotanni daga jihar ta Edo sun nuna cewa Hon. Agbebaku ya sauka daga kujerar ne bayan wasu ‘yan majalisa sun shirya tsige shi
  • Mai taimaka masa kan harkokin yaɗa labarai, Ivy Ebojele, ta tabbatar da murabus ɗin amma babu wani cikakken bayani kawo yanzu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Edo, Nigeria - Rahotannin da muke samu da safiyar yau Litinin, 17 ga watan Agusta, 2026 sun nuna cewa Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Edo, Rt. Hon. Blessing Agbebaku, ya yi murabus daga mukaminsa.

Bayanai sun nuna cewa Hon. Agbebaku ya dauki matakin sauka daga kujerarsa ne bayan wasu ‘yan majalisar sun shirya tsige shi.

Blessing Agbebaku.
Kakakin majalisar dokokin jihar Edo, Rt. Hon. Blessing Agbebaku a bakin aiki Hoto: Blessing Agbebaku
Source: Facebook

Mai taimaka wa Agbebaku kan harkokin yaɗa labarai, Ivy Ebojele, ce ta tabbatar da murabus ɗin, kamar yadda jaridar The Nation ta ruwaito

Kara karanta wannan

Miji ya sakawa matarsa fetur, ya banka mata wuta ta kone

Ebojele ta ce za a bayyana ƙarin bayanai kan dalilin da kuma yadda murabus ɗin ya kasance daga baya.

Ku saurari karin bayani...

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262