Bayanin da Sheikh Gumi Ya Yi kan Amfanin da Kudin Gwamnati don Shirya Auren Gata

Bayanin da Sheikh Gumi Ya Yi kan Amfanin da Kudin Gwamnati don Shirya Auren Gata

  • Sanannen malamin addinin Musulunci, Dr Ahmad Gumi ya yi magana kan amfani da kudin gwamnati wajen gudanar da auren gata da wasu gwamnatoci ke gudanarwa a jihohinsu
  • Malamin addinin ya kare shirin auren gata na Kano bayan wasu sun soki yadda ake amfani da kudaden gwamnati wajen gudanar da shi
  • Sheikh Gumi ya ce taimaka wa matasan da ke tsananin bukatar aure na daga cikin nauyin da gwamnati ke da shi

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Kaduna - Sanannen malamin addinin Musulunci da ke jihar Kaduna, Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi, ya kare amfani da kudaden gwamnati wajen gudanar da auren gata.

Sheikh Gumi ya bayyana cewa hakan wani bangare ne na halastaccen kuma nagartaccen shugabanci a jihar da ke tafiyar da harkokinta bisa Shari’a.

Sheikh Gumi ya yi magana kan auren gata
Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi ya gabatar da karatu Hoto: Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi
Source: Facebook

Sheikh Ahmad Gumi ya bayyana hakan ne a shafinsa na Facebook a ranar Alhamis, 13 ga watan Agustan 2026.

Kara karanta wannan

Gwamntin Tinubu na neman 'ƙaryata' rahoton da ƙasar Amurka ta fitar kan Najeriya

Malamin addinin ya bayyana hakan ne yayin da yake mayar da martani kan sukar da ake yi wa auren gata da gwamnatin jihar Kano ta gudanar.

Me Sheikh Gumi ya ce kan auren gata?

Sheikh Gumi ya ce irin wannan shiri ya dace a jihar da dokokin Musulunci da na gwamnati suka haramta karuwanci, zina da lalata.

“A jihar da ke tafiyar da harkokinta bisa Shari’a, inda dokokin Allah da na gwamnati suka haramta karuwanci, zina, lalata da fasikanci, amfani da kudin gwamnati wajen tallafa wa auren matan da suka fi yawan mazan da suka cancanci aurensu, ko kuma duk wani matashi da ke tsananin bukatar aure, wani bangare ne na halastaccen kuma nagartaccen shugabanci,” in ji shi.

Gumi ya bayyana nauyin da ke kan gwamnati

Malamin addinin Musuluncin ya ce taimaka wa matasan da ke tsananin bukatar aure ya kamata a dauke shi a matsayin wani bangare na nauyin da gwamnati ke da shi, musamman a al’ummar da ake tafiyar da harkokinta bisa ka’idojin Shari’a.

Kara karanta wannan

Babbar magana: Atiku ya yi gargadi mai zafi ga INEC, Tinubu kan zaben Osun

Kalaman Gumi sun zo ne a daidai lokacin da ake ta sukar shirin auren gata na jihar Kano, inda wasu ke tambayar dalilin amfani da kudaden gwamnati wajen gudanar da shirin.

Sai dai Sheikh Gumi ya dage cewa ya kamata a fahimci manufar shirin ne bisa la’akari da dokoki da kuma yanayin zamantakewar al’ummar jihar da ke tafiyar da harkokinta bisa Shari’a.

Ya ce idan wasu halaye sun haramta a karkashin dokokin Allah da na gwamnati, to sa hannun gwamnati wajen tallafa wa auren da ya halasta za a iya kallonsa a matsayin matakin da ya dace da kyakkyawan shugabanci.

Sheikh Gumi ya yi tsokaci kan auren gata
Malamin addinin musulunci, Sheikh Ahmad Abubakar Mahmud Gumi Hoto: Dr. Ahmad Abubakar Mahmud Gumi
Source: Facebook

Auren gata: Gwamnatin Kano ta mika bukata ga malamai

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnatin jihar Kano karkashin jagorancin Gwamna Abba Kabir Yusuf, ta ba da umarni ga limaman masallatan Juma’a kan auren gata.

Gwamnatin ta umarci malaman su yi amfani da wa’azinsu wajen karyata bayanan ƙarya game da shirin aurar da jama’a.

Ta ce shugabannin addini, musamman limamai da malaman Musulunci, suna da muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da dakile yaɗuwar bayanan ƙarya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng