Gwamnatin Najeriya
Dokar 'yan sandan jihohi ta tanadi iyakoki da aka sanya wa gwamnoni domin hana su amfani da 'yan sandan jihohi domin cimma manufar siyasa ko wata manufa.
Surutu ya yi yawa a kan canza khaki zuwa atamfa ga masu NYSC. Ministan matasan Najeriya ya tabbatar da cewa misali kurum ya bada da yake bayanin sauyin da aka kawo.
Prince Adeniyi Adeyemi ya dage cewa nadin da aka ba shi na shugaban wata hukuma ta gaskiya ne duk da zargin jabun takardu da rike mukamin da ya ke yi.
Kasar Amurka ta janye yawancin dakarunta daga aikin yaƙi da ta'addanci a Tafkin Chadi, amma za ta ci gaba da musayar bayanan sirri da Najeriya a gaba.
Ministan Ayyuka, David Umahi, ya ce yana baƙin ciki idan mutane suna cin mutuncin Shugaba Tinubu saboda jajircewarsa wajen gina manyan ababen more rayuwa.
Olusegun Obasanjo ya ce ba ya fatan sake faruwar yakin basasa a Najeriya. Ya ce abin tsoro shi ne har yanzu ba magance abubuwan da suka haifar da yakin ba.
Fadar shugaban kasa ta zargi Adeniyi Adeyemi da kafa ma'aikatar bogi a Najeriya ba tare da sanin shugaban kasa Bola Tinubu da sauran hukumomin Najeriya ba.
Rahotanni sun nuna cewa bankin duniya zai ba shugaba Bola Tinubu bashi dala biliyan 1.25 a madadin Najeriya. Kudin ya kusa kai Naira tiriliyan 2.
A labarin nan, za a ji cewa masu kasuwancin man fetur a karkashin kungiyar IPMAN na shirin daukar mataki idan gwamnati ta nemi a kayyade farashin fetur.
Gwamnatin Najeriya
Samu kari