Matakin da Gwamna Bago Ya Dauka kan Mutuwar Mutane 37 a Hannun NSCDC
- Gwamnatin Neja ta soke gangamin APC da aka shirya gudanarwa a Minna bayan mutuwar mutane 37 da ke tsare a hannun NSCDC
- Gwamna Umaru Bago ya ayyana kwanaki uku na zaman makoki domin girmama waɗanda suka mutu tare da jajanta wa iyalansu
- Gwamnatin jihar ta rufe wurin haƙar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da ke MiOshishi, inda ta ce ana gudanar da ayyukan ba tare da isassun kayan tsaro ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Neja - Gwamnatin Jihar Neja ta soke gangamin siyasar All Progressives Congress (APC) da aka shirya gudanarwa ranar Asabar a Minna, babban birnin jihar.
An ɗauki matakin ne bayan mutuwar mutane 37 da rahotanni suka ce suna tsare a hannun Hukumar NSCDC a jihar Neja.

Source: Twitter
Bago ya ayyana zaman makoki
Tashar Channels tv ta ce hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labaran gwamnan Neja, Bologi Ibrahim, ya fitar.
Gwamna Umaru Bago ya jajanta wa iyalan waɗanda suka mutu, sannan ya kuma ayyana kwanaki uku na zaman makoki domin girmama mamatan.
Gwamnatin jihar ta ce an soke gangamin ne saboda munanan abubuwan da suka faru, da kuma nuna girmamawa ga mamatan da iyalansu.
Gangamin APC da aka soke zai kasance wani ɓangare na ayyukan siyasar jam’iyyar a jihar, kuma an shirya gudanar da shi a Minna a wannan ƙarshen mako.
Gwamnati ta umarci hukumomi su dauki mataki
Gwamnatin Neja ta kuma umarci hukumomin da abin ya shafa da su ɗauki matakan da suka dace dangane da lamarin.
Bago ya kuma sanar da rufe wurin haƙar ma’adinai da ke yankin MiOshishi, yana mai cewa ana gudanar da ayyukan haƙar ma’adinan ba tare da amfani da fasahar da ta dace da kayan aikin kare lafiyar ma’aikata ba.
Bago ya yi kira ga matasa su guji rikici
Gwamnan ya yi kira ga jama’a da su kwantar da hankalinsu bayan kai gawarwakin waɗanda suka mutu zuwa ɗakin ajiye gawarwaki, lamarin da ya ce ya jawo tashin hankali da martanin wasu matasa.
“Muna kira ga dukkan matasanmu da su guji tashin hankali. Ba zai dawo da waɗanda suka mutu ba. A ƙarshe zai jawo mana babbar asara,” in ji Bago.
Ya buƙaci matasan jihar su guji ɗaukar doka a hannunsu, yana mai cewa tashin hankali ba zai magance matsalar da ta faru ba.
Ana shirya sunayen mamatan
Bago ya ce gwamnatin jihar tana tattara jerin sunayen waɗanda suka mutu domin samun damar gano iyalansu da kuma tuntuɓar su.
Ya sake mika ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan, tare da addu’ar Allah Ya jiƙan waɗanda suka rasu, Ya kuma ba iyalansu da sauran ’yan uwansu haƙurin jure wannan babban rashi.

Source: Original
An dakatar da kwamandan NSCDC
A wani labarin kuma, kun ji cewa dakatar da kwamandan rundunar NSCDC na Jihar Neja, Suberu Aniviye, sakamakon mutuwar wasu da ake zargin masu haƙar ma’adinai ba bisa ƙa’ida ba.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ya bayar da umarnin dakatar da kwamandan nan take tare da gudanar da cikakken bincike kan lamarin.
Asali: Legit.ng

