'Yan Bindiga Sun Kai Hari a Kwaleji, an Yi Awon Gaba da Dalibai

'Yan Bindiga Sun Kai Hari a Kwaleji, an Yi Awon Gaba da Dalibai

  • An ce wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace ɗalibai takwas na Gateway ICT Polytechnic a jihar Ogun
  • Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne bayan da maharan suka kai hari gidan da ɗaliban ke zaune a Ipara
  • Hukumar makarantar ta soke jarabawar da aka shirya yi bayan aukuwar lamarin na sace dalibai da ba su san hawa ba, ba su san sauka ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Jihar Ogun - An ce wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun sace ɗalibai takwas na Gateway ICT Polytechnic, Saapade (GAPOSA).

'Yan bindigan sun sace daliban ne bayan sun kai hari gidan da ɗaliban ke zaune a Ipara, ƙaramar hukumar Remo North ta jihar Ogun.

'Yan bindiga sun sace dalibai a Ogun
Taswirar jihar Ogun, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Wani ɗalibi a makarantar da ya yi magana da jaridar Tribune Online bisa sharadin a sakaya sunansa ya ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 9:00 na daren ranar Laraba, 29 ga watan Yulin 2026.

Kara karanta wannan

Hayaniya ta kaure kan rabon lasisin shigo da fetur Najeriya

Majiyar ta ce masu garkuwar sun tafi da ɗalibai takwas a yayin harin.

Makaranta ta soke jarabawa

Bayan aukuwar lamarin, an ce hukumar makarantar ta sanar da soke jarabawar kwamfuta da ta rubutu da aka shirya gudanarwa a ranar Alhamis.

A wata sanarwa da hukumar makarantar ta fitar, ta ce:

“SANARWA GA DUKKAN ƊALIBAI. Bayan mummunan lamarin da ya faru jiya, an soke jarabawar yau."
"Sai dai za a gudanar da jarabawar gobe kamar yadda aka tsara. Idan aka samu wani sauyi game da jarabawar gobe, za a sanar da ɗalibai cikin gaggawa."
"A yanzu, ana ƙarfafa dukkan ɗalibai su kwantar da hankulansu, su kasance masu kyakkyawan fata tare da ci gaba da shirye-shiryen jarabawarsu. Muna fatan za a warware lamarin cikin gaggawa. Mun gode da fahimta da haɗin kai.”

’Yan sanda sun tura jami’ai

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Ogun, DSP Oluseyi Babaseyi, ya tabbatar wa jaridar cewa sun samu rahoton sace wasu mutane a yankin Ipara.

Kara karanta wannan

An fadi sunayen 'yan ta'adda 5 da aka kama suna sace dalibai da aka je kotu

Sai dai kakakin ’yan sandan bai tabbatar da adadin mutanen da aka sace ba.

Ya ce rundunar ’yan sandan Najeriya ta tura jami’anta yankin cikin gaggawa, musamman jami’an sashen yaƙi da garkuwa da mutane da sashen yaƙi da manyan laifukan tashin hankali da sauran rundunonin musamman.

Da aka tuntuɓi jami’in hulɗa da jama’a na makarantar, ya yi alƙawarin sake tuntuba domin yin ƙarin bayani kan lamarin.

Sai dai har zuwa lokacin wallafa wannan rahoto, ba a samu ƙarin bayani daga hukumar makarantar ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng