Yar Makaranta
A labarin nan, za a ji gwamnatin tarayya ta bayar da tabbacin cewa ta ceto baki daya daliban makarantar Papiri da suka rage a hannun 'yan ta'adda.
Yara huɗu sun mutu a jihar Kogi bayan wata mota ta afka cikin kogi da ɗaliban da take ɗauka zuwa makaranta. Al’umma sun yi zanga-zanga kan rashin makaranta a Egbolo.
Fadar shugaban kasa ta kare kalaman da Bola Tinubu ya yi na neman Goodluck Jonathan ya yi murabus daga kujerar shugaban kasa kan sace yan mata a Chibok.
Jagoran jam'iyyar NNPP, Buba Galadima ya ce abin kunya ne yadda gwamnonin Arewa suke rufe makarantu saboda barazanar rashin tsaro da sace dalibai da malamai.
A labarin nan, za a ji rundunar ƴan sandan Delta ta aika da jami'ai wata makarantar mata a jihar bayan an samu rahoton harbi da ake tsammanin harin ƴan bindiga ne.
Gwamnatin Gombe ta umarci makarantun jihar su kulle zuwa ranar Juma'a. An umarce su da su yi jarrabawa cikin gaggawa domin sallamar dalibai saboda barazanar tsaro
A labarin nan, za a ji cewa gwamnatin Bauchi ta ce a rufe makarantun firamare, sakandare da na gaba da sakandare mallakkinta da masu zaman kansu saboda sace dalibai.
Dalibai 50 daga makarantar St. Mary’s Papiri sun tsere daga hannun ’yan bindiga a Niger, yayin da daruruwan sauran dalibai da ma’aikata ke tsare a daji.
Yara sun fara barin FGGC Bwari bayan umarnin gwamnati na rufe makarantu 47 saboda barazanar tsaro da yawaitar sace dalibai a Arewa. Iyaye sun yi martani kan hakan.
Yar Makaranta
Samu kari