Yadda Daliban Jami’ar Jos Suka Hallaka Matashi Kan Zargin Sata Wayar iPhone

Yadda Daliban Jami’ar Jos Suka Hallaka Matashi Kan Zargin Sata Wayar iPhone

  • Wani matashi wanda ya kammala jami'ar Jos, ya rasu bayan wasu da ake zargi sun yi masa dukan tsiya kan zargin satar iPhone
  • Rundunar 'yan sandan Plateau ta kama mutane uku da ake zargi, bayan bidiyon yadda aka doke marigayin da katako da bulala ya bazu sosai
  • 'Yan sanda sun ce maimakon kai korafi ga hukuma, wadanda ake zargi sun dauki doka a hannunsu, tare da gargadin jama'a su guji daukar doka a hannu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Jos, Plateau - Rundunar ƴan sanda a jihar Plateau sun cafke wasu daliban Jamiar Jos kan zargin kashe wani matashi.

Matashi mai shekaru 25 mai suna Ibrahim Mbaya, wanda aka fi sani da Ibee, ya mutu bayan wasu da ake zargi sun yi masa dukan tsiya kan zargin satar waya.

Kara karanta wannan

Yan sanda sun yi musayar wuta ana tsaka da garkuwa da mutane a hanyar Kano

An kama wasu da ake zargin sun hallaka matashi a Jos
Ibrahim Mbaya da wasu da ake zargin sun hallaka shi a Jos. Hoto: Bell Bill.
Source: Facebook

Daily Trust ta ce lamarin ya faru ne a wani gida da ke wajen harabar Jami'ar Jos, bayan yankin City of David da ke kan hanyar Ring a Jos.

Yadda aka zargi Mbaya da satar waya

Rahotanni sun ce Mbaya ya halarci wani taro a harabar jami'a kafin ya kwana a gidan wani abokinsa saboda dare ya yi, ana kuma cewa yana kokarin kammala wani sauran al'amari na karatunsa a jami'ar.

Da safe, abokan da suke tare da shi sun ce wata wayar iPhone ta bace. Saboda su kadai ne ke cikin dakin, suka zarge shi da satar wayar tare da fara dukansa.

Bidiyon da ya bazu a shafukan sada zumunta ya nuna yadda ake dukansa da katako da bulala, tare da azabtar da shi har sai da ya rasa hayyacinsa. Daga bisani ya mutu sakamakon raunukan da ya samu.

Rundunar 'yan sandan Plateau ta tabbatar da kama mutane uku da ake zargi da hannu a lamarin. Kakakin rundunar, SP Alabo Alfred, ya ce an mika su zuwa Sashen Binciken Manyan Laifuka domin ci gaba da bincike.

Kara karanta wannan

Yan sandan MOPOL sun nemi agajin Sufeton Ƴan sanda watanni 7 da hana su alawus

A cewarsa, 'yan sanda sun samu rahoto daga wani mutumin kirki bayan an kai marigayin Asibitin Koyarwa na Jami'ar Jos cikin halin rashin sani.

Likita ya tabbatar da rasuwarsa, sannan aka ajiye gawarsa a dakin ajiyar gawa domin binciken gawa, cewar Sahara Reporters.

Daliban Jami'a sun kashe matashi a Jos
Taswirar jihar Plateau da ke Arewacin Najeriya. Hoto: Legit.
Source: Original

An cafke wasu da ake zargi

Binciken farko ya nuna cewa daya daga cikin wadanda aka kama, Emmanuel Newyear, shi ne aka gani a bidiyon yana dukan marigayin da wani katon katako, haka kuma hotuna sun taimaka wajen gano wadanda ake zargi.

'Yan sandan sun ce wadanda ake zargin sun amsa cewa sun yi zargin Mbaya ya saci iPhone 12. Sai dai maimakon su kai karar lamarin ga jami'an tsaro, sun dauki doka a hannunsu har lamarin ya kai ga mutuwarsa.

Rundunar ta yi gargadin cewa kowa da ake zargi da laifi yana da hakkin a bi masa ka'idojin shari'a. Ta bukaci jama'a su daina hukuncin kangaroo, su rika kai rahoton laifi ga hukumomin da abin ya shafa.

An kashe iyalan Fasto a Plateau

A wani labarin, an ji cewa gwamnatin Amurka ta yi Allah-wadai da mummunan kisan da aka yi wa wasu daga cikin iyalan Fasto Ezekiel Dachomo a jihar Plateau.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga kusan 200 sanye da kayan sojoji sun yi ta'asa a jihar Sokoto

Ma'aikatar Harkokin Wajen Amurka ta ce dole ne a hukunta masu hannu a kisan tare da ƙara tsaurara matakan tsaro ga Kiristoci da sauran al'ummomin da ke cikin haɗari.

Lamarin ya haifar da martani daga masu amfani da kafafen sada zumunta, inda wasu suka nuna shakku kan matsayar gwamnatin Amurka kan matsalar tsaro a Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.