Bauchi: Bala Mohammed Ya Yi Garambawul a Majalisar Zartarwa, Ya Sauke Kwamishinoni 2
- Gwamnan Bauchi Bala Mohammed ya yi ƙaramin garambawul a majalisar zartarwar jihar inda ya raba wasu daga cikin kwamishinoninsa da kujerunsu
- Haka kuma an samu 'daya daga cikin kwamishinoninsa ya yi murabus, kuma gwamnan ya amince da ajiye mukaminsa da ya yi nan take
- A yanzu haka, an tura sunayen sababbin waɗanda aka zaɓa zuwa Majalisar Dokokin Bauchi domin tantancewa da amincewa da su
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
Jihar Borno – Gwamnan Bauchi, Sanata Bala Mohammed, ya amince da yin ƙaramin garambawul a majalisar zartarwar jihar, inda kwamishinoni biyu suka bar mukamansu, sannan ya amince da murabus na wani kwamishina.
Mai ba gwamnan shawara na musamman kan harkokin yaɗa labarai da hulɗa da jama'a, Mukhtar Gidado, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Juma'a 17 ga watan Yuli, 2026.

Source: Twitter
Nigerian Tribune ta wallafa cewa ya ce matakin na daga cikin ƙoƙarin gwamnatin jihar na ƙara inganta shugabanci da kuma samar da ingantaccen aiki ga al'ummar Bauchi.
Dalilin gwamnatin Bauchi na garanbawul
A cewar sanarwar, an dakatar da Kwamishinan Kasuwanci, Masana'antu da Zuba Jari, Mohammed Salis Gamawa, da tsohon Kwamishinan Ilimi, Dakta Lawal Rimin Zayam, wanda daga baya aka mayar da shi Ma'aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha.
Haka kuma, gwamnan ya amince da murabus ɗin tsohon Kwamishinan Raya Karkara da Ayyuka na Musamman, Faruk Mustapha.
Gidado ya ce:
"A matsayin wani ɓangare na sauye-sauyen da aka yi, Kwamishinan Kasuwanci, Masana'antu da Zuba Jari, Mohammed Salis Gamawa, da tsohon Kwamishinan Ilimi wanda daga baya aka mayar da shi Ma'aikatar Wutar Lantarki, Kimiyya da Fasaha, Dakta Lawal Rimin Zayam, sun daina kasancewa cikin majalisar zartarwar jihar nan take. Haka kuma gwamnan ya amince da murabus na tsohon Kwamishinan Raya Karkara da Ayyuka na Musamman, Faruk Mustapha."

Kara karanta wannan
Gwamna ya zakulo samari da zawarawa 300, zai masu auren gata da sadakin N250000 a Kebbi
An tura sunayen yan majalisa Bauchi
Sanarwar ta kuma bayyana cewa Gwamna Bala Mohammed ya aika da sunayen waɗanda aka zaɓa domin maye gurbin waɗanda suka fita, tare da sauran waɗanda za su cike guraben da suka samu a majalisar zartarwar jihar, zuwa Majalisar Dokokin Jihar Bauchi.

Source: Facebook
Ana sa ran majalisar za ta tantance su tare da ba su amincewar da doka ta tanada kafin su fara aiki. Gidado ya ce matakin ya dace da manufar gwamnatin jihar ta tabbatar da ci gaba da gudanar da mulki cikin inganci da kuma ba tare da tangarda ba.
Ya ce:
"Domin tabbatar da dorewar aiki da ingancin gudanar da mulki, an tura sunayen waɗanda aka zaɓa domin maye gurbin waɗanda suka fita, tare da sauran masu neman cike guraben da suka samu sakamakon ficewar wasu kwamishinoni a baya, zuwa Majalisar Dokokin Jihar Bauchi domin tantancewa da amincewa."
Gwamna Bala Mohammed ya gode wa kwamishinonin da suka bar mukamansu bisa gudummawar da suka bayar wajen ci gaban jihar Bauchi.
An rubuta wa gwamnan Bauchi wasika
A baya, mun kawo labarin cewa gwamna Bala Mohammed na jihar Bauchi ya samu budaddiyar wasika daga wajen dansa, Shamsudeen Bala Mohammed inda ya ja hankalinsa game da ci gaban al'umma.
Yaron gwamnan ya yaba kan irin ayyukan raya kasa da nasararin da Gwamnan jihar Bauchi ya samu cikin shekaru bakwai a kan mulki sai dai, Shamsudeen ya kuma jawo hankalin Bala Mohammed kan wasu abubuwa.
Shamsudeen ya bayyana cewa ya rubuta wasikar ne domin bayyana ra'ayinsa cikin girmamawa, tare da nuna damuwa kan halin da ake ciki a Bauchi domin a kara samun ci gaban al'ummar jihar Bauchi.
Asali: Legit.ng

