Cikakken Jerin Jami'an Tsaron da Suka Sadaukar da Ransu wajen Ceto Dalibai a Oyo
- Majalisar Dattawa ta bayyana sunayen jami'an tsaro da suka rasa rayukansu yayin aikin ceto dalibai da malamai da aka sace a jihar Oyo
- Aikin ya kawo ƙarshen kwanaki 56 da waɗanda aka sace suka shafe a hannun 'yan ta'adda, inda aka ceto yawancinsu cikin nasara
- Sojoji da 'yan sanda uku sun mutu, wani soja kuma ya jikkata yayin da aka kama mutane takwas da ake zargi da ta'addanci
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
FCT, Abuja - An bayyana sunayen jami'an tsaro da suka sadaukar da rayukansu yayin aikin soji da ya kawo ƙarshen kwanaki 56 da dalibai da malamai da 'yan ta'adda suka sace a ƙaramar hukumar Oriire da ke jihar Oyo.
Bayyanar sunayen ta sake fito da irin sadaukarwar da jami'an tsaron suka yi wajen ceto waɗanda aka sace, duk da cewa aikin ya yi sanadiyyar mutuwar wasu jami'ai da kuma jikkatar wani soja.

Source: Twitter
Jaridar Daily Trust ta ce Majalisar Dattawa ce ta bayyana sunayen jami'an yayin da take karrama su saboda irin rawar da suka taka wajen ganin an ceto waɗanda aka sace.
Sai dai duk da wannan rashi, an samu nasarar ceto mafi yawan dalibai da malaman da aka yi garkuwa da su, tare da cafke waɗanda ake zargi da hannu a lamarin.
Sunayen jami'an da suka rasa rayukansu
Jami'an tsaron da suka mutu yayin wannan aiki sun haɗa da:
- Laftanar F. A. Isaac na rundunar sojojin Najeriya
- Private Silas Musa na Bataliya ta 81 ta rundunar sojojin Najeriya
- Sajan Abena John Jerome na rundunar 'yan sandan Najeriya
Haka kuma, Lance Corporal Adamu Hussain na Bataliya ta 81 ya samu raunuka a musayar wuta, amma ya tsira bayan an yi masa magani.
Yadda aikin ceto ya gudana
Shugaban masu rinjaye na Majalisar Dattawa, Opeyemi Bamidele, ya ce an fara aikin ne bisa sahihan bayanan sirri bayan Shugaba Bola Tinubu ya umarci hukumomin tsaro da su tattara dukkanin kayan aiki da ƙarfin da ake da su domin tabbatar da an sako waɗanda aka sace ba tare da wani sharaɗi ba.
A cewar Opeyemi Bamidele, aikin ya ɗauki fiye da kwanaki 50 kafin ya kai ga nasarar ceto dalibai da malaman da aka yi garkuwa da su.
Ya ƙara da cewa jami'an tsaro sun kama mutane takwas da ake zargi da hannu a satar mutanen, tare da kashe wasu daga cikin 'yan ta'addar yayin aikin, jaridar The Punch ta kawo labarin.
Sai dai ya bayyana alhininsa kan mutuwar ɗaya daga cikin malaman da aka sace, wanda ya rasu tun yana hannun 'yan ta'addan kafin a kammala aikin ceto.

Source: Original
Fadar shugaban kasa ta soki Gwamna Makinde
A wani labarin kuma, kun ji cewa fadar shugaban kasa ta caccaki gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde, kan kiran da ya yi a gudanar da bincike karkashin Majalisar Dinkin Duniya (UN) game da sace dalibai da malamai a jihar.
Fadar shugaban kasa ta bayyana cewa kiran da kalaman gwamnan abu ne wanda bai kamata ba, inda ta ce yana kokarin sanya siyasa a lamarin.
Asali: Legit.ng

