Gwamnati Ta Bayyana Dalilin da Ya Sa NIN ba Ta Gano Masu Garkuwa da Mutane
- Hukumar bayar da shaidar 'dan kasa ta NIMC ta y karin haske a kan dalilin da ya sa ake gaza bibiyar 'yan ta'adda da sauran masu garkuwa da mutane
- Hukumar ta bayyana cewa NIN tsarin tantance mutum ne, ba kayan leƙen asiri ko bibiyar mutanen kasar nan da ke da lamabar shaidar ba
- Ta jaddada tsarin da za a iya amfani da ita wajen gano masu aikata laifi ta lambar shaidar dan kasa da su suka mallaka, domin ba aikinta kada ba ne
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
A'isha Ahmad edita ce a sashen Hausa na Legit. Tana da ƙwarewa wajen rubutun labarai da rahotanni tsawon shekaru uku. Ta kware a kawo rahotannin, al'amuran da su ka shafi mata da yara da siyasa.
FCT Abuja – Babbar Darakta Janar ta Hukumar Kula da Shaidar Ɗan Ƙasa ta Kasa (NIMC), Abisoye Coker-Odusote, ta bayyana dalilin da ya sa ba a iya gano masu garkuwa da mutane da 'yan ta'adda ta hanyar Lambar Shaidar Ɗan Ƙasa (NIN).
Ta bayyana haka ne duk da muhimmancin tsarin wajen inganta tsaron Najeriya, wanda kuma aka umarci kowanne dan kasa ya tabbata ya mallaka.

Source: Getty Images
Da take magana a shirin Sunday Politics na tashar Channels Television, Coker-Odusote ta ce sau da yawa masu garkuwa da mutane kan yi amfani da wayoyin mutanen da suka sace maimakon layukansu da aka yi wa rajista.
Dalilin da NIN ba ya kama yan ta'adda
Jaridar Punch ta wallafa cewa Abisoye Coker-Odusote ta kara da cewa akwai wata fahimta da ke cewa wasu daga cikin masu garkuwa da mutane na iya kasancewa ba 'yan Najeriya ba ne, kuma ana iya shigo da su ƙasar awanni 48 zuwa 72 kafin su aikata laifin.
A cewarta:
"Akwai wata fahimta cewa watakila waɗannan masu garkuwa da mutane ba 'yan Najeriya ba ne, ana shigo da su ƙasar ne sa'o'i 48 ko 72 kafin a aikata satar mutane. Ba ina tabbatar da haka ba ne, amma idan hakan ne, to ba za su kasance cikin bayananmu ba. Waɗannan na daga cikin yiwuwar da muke gani."
Ta jaddada cewa duk da muhimmancin NIN a tsarin tantance mutane da tsaron ƙasa, masu laifi kan yi amfani da dabaru da ke sa a yi wahalar gano su, ciki har da amfani da wayoyi na waɗanda suka sace.
Ba a leken asiri da NIN
Hukumar ta jaddada cewa NIN lamba ce ta musamman mai lambobi 11 da NIMC ke bai wa 'yan Najeriya da kuma baƙin da ke zaune a ƙasar bisa doka, kamar yadda Dokar NIMC ta shekarar 2007 ta tanada.

Source: Twitter
Gwamnatin Tarayya ta mayar da NIN wani muhimmin ɓangare na tsarin tsaro ta hanyar wajabta haɗa layukan waya da NIN domin ƙarfafa tantance mutane, sauƙaƙa bincike da kuma yaƙi da laifuffuka.
Sai dai NIMC ta nanata cewa NIN tsarin kula da bayanan shaidar mutum ne kawai, ba tsarin bibiyar mutane ko leƙen asiri ba, kuma gano masu laifi na buƙatar haɗin gwiwar hukumomin tsaro, kamfanonin sadarwa da sauran hukumomin da abin ya shafa.
An zauna kan yaki da yan ta'adda
A baya, mun wallafa cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi babban taron tsaro da shugabannin rundunar soji da hukumomin leken asiri a fadar shugaban kasa saboda karuwar matsalolin tsaro.
Taron ya zo ne bayan dakarun Najeriya sun hallaka 'yan ta'adda kusan 300 a jihohin Zamfara da Katsina tare da kashe wani babban kwamandan 'yan bindiga yayin da ake kokarin kakkabe rashin tsaro a kasar nan.
Haka kuma ya zo bayan an kai wa sansanin soja na Mairari hari a Arewa maso Gabas, kuma an kai fiye da hare-hare 13 kan sansanonin soja a 2026 kadai da karin wasu hare-hare a Arewacin Najeriya.
Asali: Legit.ng


