Tsohon Minista Ya Tona Asirin ‘Yan Majalisar da Suka Nemi Cin Hancin N200m
- Solomon Dalung ya zargi ‘yan majalisa da neman ya biya cin hanci wajensa a shekarun da yake minista a gwamnati
- ‘Dan siyasar ya yi shekaru kusan hudu a matsayin ministan matasa da wasanni a mulkin Muhammadu Buhari
- Domin majalisa ta amince da kasafin kudinsu, Dalung ya ce wasu abokan aikinsa sun rika biyan cin hancin kudi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M. Malumfashi ya shafe shekaru 10 yana kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada
Abuja - Tsohon ministan harkokin matasa da wasanni, Solomon Dalung ya yi zargin cewa ‘yan majalisa sun nemi cin hanci daga wajen shi.
Barista Solomon Dalung ya ce ‘yan majalisar Najeriyan sun bukaci ya biya cin hanci na N200m lokacin da ya nemi kare kasafin kudin ma’aikatarsa.

Source: Getty Images
Solomon Dalung ya zargi majalisa da cin hanci
A ranar Laraba ne jaridar Daily Trust ta rahoto tsohon ministan yana wannan bayani a wani jawabi da ya fitar yana tuna lokacin da yake ofis.
Solomon Dalung wanda ya yi minista a mulkin marigayi shugaba Muhammadu Buhari ya nuna yadda rashin gaskiya ta yi kane-kane a Najeriya.
Dalung ya shaida cewa an gabatar masu da wannan bukata ne jim kadan bayan ya je gaban ‘yan majalisar tarayya ya kare kasafin kudin shi.
Jim kadan bayan an yi hakan, ‘yan majalisar suka nemi ya biya N200m, cin hancin da bai da alaka da amincewa da kudin da ma’aikatarsa za ta kashe.
"Na duba takardar kasafin kudin da yake gaba na, na fada masu ban ga bangaren da aka rubuta ‘cin hanci’ ba.
Na fada wa kwamitin cewa tunda babu wannan bangare a kasain kudin ma’aikatar, ban san ina ku ke so in samo N200m ba."
- Solomon Dalung
'Yan majalisar sun hakura sun rabu da minista
Tsohon ministan ya ce da wannan magana ne ya rufe bakin ‘yan kwamitin majalisar tarayyar.
Sai kawai suka ce mani, ‘Shikenan minista, mun yi maka uzuri. Za mu dangana da Babban sakatare’
Mista Dalung wanda shi kan shi lauya ne ya ce rawar da yake taka wa wajen kare kasafin kudi ya ragu sosai bayan wannan takaddama.
A cewarsa da zarar ya gabatar da kasafin kudinsa na shekara, ‘yan majalisa sukan ce ya yi tafiyarsa, sai a zauna da manyan jami’an ma’aikatarsa.
Ya ce daga baya ya gano cewa ba ma’aikatar matasa da wasanni kurum abin ya shafa ba, dole wasu ministoci suka rika biye wa ‘yan majalisar.

Source: Getty Images
Wasu ministoci sun rika ba majalisa cin hanci
Domin ganin an yi na’am da kasafin kudinsu, ya ce wasu ministoci har na kusa da Muhammadu Buhari sun rika bada cin hancin miliyoyi.
A jawabinsa, babban 'dan siyasar bai kama sunayen wadanda suka bada ko suka karbi hancin ba. Labarin nan ya bayyana a tashar Trust Radio.
Zuwa yanzu majalisa ba ta tanka 'dan adawan ba, kuma shi ma bai kawo wasu hujjoji da za su tabbatar da wannan zargi mai nauyi da ya yi ba.
Tsohon minista zai yi shari'a da hukumar ICPC
An ji labari kashin tsohon ministan Bola Tinubu zai bushe, lauyan EFCC ya shigar da karar shi a kotu saboda wasu zargi shida da ake yi masa
Za gurfanar da tsohon ministan kimiyya da fasaha, Chief Uche Geoffrey Nnaji saboda samun shi da amfani da takardun bogi, zargin da ya karyata.
Hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa ta ICPC ta shigar da zarge-zargen laifuffuka gaban Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja a kan Uche Nnaji.
Asali: Legit.ng


