Abun Al Ajabi
Rundunar 'yan sanda ta kama mutane hudu bisa zarginsu da hannu a damfar wani tsohon janar na sojan Najeriya da sunan ministan Abuja, Nyesom Wike a Abuja.
Gwamnan jihar Delta, Sheriff Oborevwori ya yi alhinin rasuwar hadiminsa, wanda ke tsare masa duk wasu ayyukan da zai yi, an ce ya rasu ne a wurin taro.
Wani dan jarida mai zaman kansa a kasar Amurka, Nathan Levins ya yi ikirarin cewa Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya rasu. Ya ce an yi zaman makoki.
Wata mata a Najeriya ta haifi jarirai hudu lokaci guda, lamarin ya jawo damuwa, saboda kudin jinya na Naira miliyan uku hakan ya jawo aka rike ta a asibiti.
An kama mutum uku bisa zargin alaka da sassan jikin gawa. An kama wani mutum bayan ya shiga makabarta zai tono gawa. Ya ce ya taba tono gawa domin yin tsafi.
Gwamnan Akwai Ibom, Pastor Umo Eno, ya yi barazanar kwace takardun sarautar sarakunanan gargajiya idan suka bari aka samu barnata kayan gwamnati a jihar.
Sanata Kawu Sumaila ya roki jama'a su guji martani ga Alhassan Ado Doguwa, yana bayyana cewa halin da yake ciki yana bukatar addu'a da goyon baya.
Hukumar EFCC ta yi martani ga wani matashi da ya yi rubutu a kafar X yana talla domin neman mai sayen ofishin hukumar EFCC a kan kudi N800m, kudin dillali N120m.
Hukumomin Kano na nuna damuwa game da rufe hanyoyi yayin sallar Juma’a, suna mayar da hankali kan inganta zaman rayuwa da kare al’umma daga cikas.
Abun Al Ajabi
Samu kari