A Karshe, Amurka Ta Janye Sojojinta daga Najeriya, Ta Sabunta Salon Alakarsu

A Karshe, Amurka Ta Janye Sojojinta daga Najeriya, Ta Sabunta Salon Alakarsu

  • Amurka ta janye yawancin dakarunta daga aikin yaƙi da ta'addanci a Tafkin Chadi, amma za ta ci gaba da musayar bayanan sirri da Najeriya
  • Janar Dagvin Anderson ya ce haɗin gwiwar bayanan sirri tsakanin Amurka da Najeriya ya taimaka wajen kashe mataimakin shugaban ƙungiyar ISIS na duniya
  • Amurka ta ce haɗin gwiwar ƙasashen Afirka wajen musayar bayanan sirri zai taimaka wajen yaƙar ta'addanci, safarar miyagun ƙwayoyi da sauran manyan laifukan ƙetare iyaka

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Washington DC, US - Amurka ta janye mafi yawan dakarunta da aka tura Najeriya domin aikin haɗin gwiwa na yaƙi da ta'addanci a yankin Tafkin Chadi.

Sai dai ta tabbatar da cewa za ta ci gaba da musayar bayanan sirri da sauran haɗin gwiwar tsaro da Najeriya.

Amurka ta janye sojojinta a Najeriay
Shugaba Bola Tinubu da Donald Trump. Hoto: Bayo Onanuga, Donald J Trump.
Source: Getty Images

Kwamandan Rundunar Sojin Sama ta Amurka a Turai da Afirka, Janar Dagvin R.M. Anderson, ne ya bayyana hakan yayin wani taro, cewar Punch.

Kara karanta wannan

Zabe na karatowa, Tinubu zai ciwo bashin dala biliyan 1.25 a bankin duniya

Ya bayyana cewa aikin sojan da aka gudanar ya ƙare, kuma yawancin sojojin Amurka da suka shiga aikin sun bar Najeriya bayan kammala aikinsu cikin nasara.

Sai dai ya ce gwamnatin Amurka za ta ci gaba da tallafa wa Najeriya ta hanyar musayar bayanan sirri, bisa buƙatar gwamnatin Najeriya domin ci gaba da yaƙi da ta'addanci.

Anderson ya ce aikin da aka gudanar a yankin Tafkin Chadi bai amfani ƙasashen yankin kaɗai ba, har ma ya taimaka wajen raunana cibiyar sadarwar ƙungiyar ISIS a duniya baki ɗaya.

Ya ƙara da cewa janye dakarun ba yana nufin kawo ƙarshen haɗin gwiwa ba, domin za a ci gaba da samar da bayanan sirri da sauran ƙwarewar da Najeriya ke buƙata.

Janar ɗin ya bayyana Najeriya a matsayin ƙasa mai ƙarfi da rundunar soji mai nagarta, yana mai cewa haɗin gwiwar ƙasashen biyu ya samar da manyan nasarori wajen yaƙar ƙungiyar ISIS.

A cewarsa, haɗuwar bayanan sirrin Amurka da ƙoƙarin sojojin Najeriya ne ya kai ga nasarar kai farmaki kan mataimakin shugaban ƙungiyar ISIS na duniya.

Ya ce Amurka ta ba Najeriya ƙwarewa da dabarun da ta koya tsawon shekaru wajen yaƙi da ta'addanci, lamarin da ya taimaka wajen cimma wannan nasara ta haɗin gwiwa.

Kara karanta wannan

Amurka ta samu nasara mafi girma cikin shekaru 25 a farmakin da ta kawo Najeriya

Anderson ya bayyana cewa wannan nasarar ta nuna muhimmancin musayar bayanan sirri fiye da dogaro da kasancewar sojojin ƙasashen waje na dogon lokaci.

Ya ce Amurka za ta ci gaba da bai wa ƙawayenta irin ƙwarewar da take da ita domin su ƙara ƙarfi wajen tunkarar ƙungiyoyin ta'addanci.

Har ila yau, ya buƙaci ƙasashen Afirka su ƙarfafa haɗin gwiwa wajen musayar bayanan sirri domin yaƙar ta'addanci, safarar miyagun ƙwayoyi da sauran laifukan da ke ƙetare iyakoki.

A cewarsa, irin wannan haɗin gwiwar ne ya taimaka wajen kama wani jirgin ruwa da ke ɗauke da tan 31 na hodar Iblis daga Kudancin Amurka zuwa gabar Tekun Yammacin Afirka.

Ya ce bayan samun bayanan sirrin, Amurka ta sanar da AFRICOM da sauran ƙawayenta, kafin wani jirgin ruwan Spain ya tare jirgin ɗauke da miyagun ƙwayoyin.

Anderson ya ce wannan shi ne mafi girman kama miyagun ƙwayoyi da aka taɓa yi a cikin teku, kuma ya nuna amfanin haɗin gwiwar ƙasashe.

Ya ƙara da cewa ci gaba da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen Afirka, ƙawayen duniya da kamfanoni masu zaman kansu zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro tare da bunƙasa tattalin arziki da jawo zuba jari.

Kara karanta wannan

Da yiwuwar Trump ya gana da Tinubu bayan hare haren da Amurka ta kawo Najeriya

A watan Fabrairun 2026 ne Amurka ta tura kusan sojoji 200 zuwa Najeriya domin tallafa wa ayyukan tattara bayanan sirri, sa ido da yaƙi da ta'addanci a yankin Tafkin Chadi.

An tura sojojin ne yayin da haɗin gwiwar tsaro tsakanin Washington da Abuja ke ƙara ƙarfi wajen yaƙar ISIS da sauran ƙungiyoyin ta'addanci a yankin.

Matakin ya biyo bayan sake ayyana Najeriya a matsayin ƙasar da ke da matuƙar damuwa ta fuskar addini da Shugaban Amurka, Donald Trump, ya yi tare da alƙawarin ƙara tallafawa yaƙi da ta'addanci.

A ranar 25 ga Disamban 2025, Amurka ta kai hare-haren sama kan sansanonin 'yan ta'adda guda biyu da ke dajin Bauni a ƙaramar hukumar Tangaza ta Sokoto.

Haɗin gwiwar ya kai kololuwa a watan Mayun 2026 lokacin da wani farmakin haɗin gwiwa tsakanin Amurka da Najeriya ya kashe Abu-Bilal Al-Minuki, mataimakin shugaban ƙungiyar ISIS, a maboyarsa da ke Borno.

Karin bayani na tafe....

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.