Jami'an ICPC Sun Cafke Tsohon Minista a Gwamnatin Tinubu a Filin Jirgin Sama

Jami'an ICPC Sun Cafke Tsohon Minista a Gwamnatin Tinubu a Filin Jirgin Sama

  • An kama tsohon ministan Kimiyya da Fasaha a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke birnin Abuja
  • Majiyoyi sun ce za a mika shi ga hukumar ICPC domin yi masa tambayoyi kan zargin amfani da takardun karatu da aka ƙirƙira
  • Majiyoyi sun ce Nnaji ya gabatar da takardun bogi ga gwamnatin tarayya, yayin da kotu ta ba ICPC umarnin kama shi da ayyana shi a matsayin wanda ake nema

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Tsohon ministan Kimiyya da Fasaha na Najeriya, Uche Nnaji, an kama shi a ranar Laraba a filin jirgin saman Nnamdi Azikiwe da ke Abuja.

Majiyoyi sun tabbatar da cewa an kama Nnaji ne bayan dawowarsa daga Enugu ta jirgin haya.

Majiyoyi masu tushe a filin jirgin sun tabbatar wa Premium Times cewa an kama Mista Uche Nnaji.

Kara karanta wannan

Uba Sani: 'Yan sanda sun kama mutum 100 kan kisan Ummulkhairi a Kaduna'

Sun ce za a mika shi ga Hukumar ICPC domin yi masa tambayoyi.

Hukumar ICPC ta dade tana neman tsohon ministan tun bayan murabus dinsa a bara. Bincike ya nuna ana zarginsa da ƙirƙirar takardun shaidar karatunsa na bogi.

A tsakiyar watan Yuni, Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta umarci ICPC ta kama Uche Nnaji. Kotun ta kuma ba hukumar izinin ayyana shi a matsayin wanda ake nema.

Hukumar ICPC ta shaida wa kotun cewa ta nemi wannan umarni ne saboda Mista Nnaji ya ƙi amsa gayyatar da aka yi masa sau da dama.

Gayyatar ICPC ta biyo bayan binciken shekaru biyu da PREMIUM TIMES ta gudanar. Rahoton ya bayyana cewa tsohon ministan ya ƙirƙira takardar digirinsa ta Jami'ar Najeriya, Nsukka da takardar NYSC.

Rahoton ya ce ya gabatar da takardun bogin ga Shugaba Bola Tinubu da Majalisar Dattawa yayin tantance ministoci a shekarar 2023 domin samun amincewa.

Binciken ya kuma nuna cewa an gabatar da takardun ga Ofishin Sakataren Gwamnatin Tarayya, Hukumar DSS da kuma Majalisar Dattawa a lokacin tantancewar.

Kara karanta wannan

Akwai dalili: Gwamnatin tarayya za ta rushe tsarin karatun sakandare na JSS da SSS

Daga baya tsohon ministan ya amince cewa Jami'ar Najeriya, Nsukka ba ta ba shi takardar digiri ba.

Da farko Mista Nnaji ya musanta cewa akwai umarnin kotu na kama shi.

Ya bayyana rahoton da aka fitar a matsayin shari'a ta kafafen yaɗa labarai.

A ranar 18 ga Yuni, Mista Nnaji ya daukaka ƙara a Kotun Ɗaukaka Ƙara da ke Abuja. Ya nemi a soke umarnin kama shi da kotun ta bayar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.