Asiri Ya Kara Tonuwa kan Kisan Malama Ummulkhairi a Hanyar zuwa Wa'azi a Kaduna
- Rundunar 'yan sandan Kaduna ta gano tre da kama karin mutum 17 da ake zargin suna da hannu a kisan Malama Ummulkhairi
- 'Yan sanda sun kuma gurfanar da wasu mutum 33 kan laifin haɗa baki da kuma taron da ba bisa ka'ida ba a MarabarJos
- Rundunar ta ce ta saki mutum 30 da aka fara kamawa tun farko bayan bincike ya nuna ba su da hannu a lamarin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Kaduna, Nigeria - Rundunar 'yan sandan jihar Kaduna ta sanar da kama tare da gurfanar da karin mutum 17 a gaban kotu kan kisan gillar da aka yi wa Malama Ummulkhairi a yankin Maraban Jos.
Rundunar ta bayyana cewa bincike kan lamarin na ci gaba, tare da alƙawarin gurfanar da duk wanda aka tabbatar yana da hannu a kisan.

Source: Getty Images
An gurfanar da karin waɗanda ake zargi
Tashar Channels tv ta ruwiato cewa a cikin wata sanarwa da kakakin rundunar, DSP Mansir Hassan, ya fitar, ya ce an gurfanar da sababbin waɗanda ake zargin a ranar 25 ga Yunin 2026.
Ya ƙara da cewa bayan kammala binciken farko, an kuma gurfanar da wasu mutum 33 bisa zargin haɗa baki da kuma shiga taron da ba bisa ƙa'ida ba dangane da lamarin.
An saki mutum 30 bayan bincike
Rundunar ta bayyana cewa mutum 30 da aka fara kama kan wannan al'amari an sake su ba tare da wani sharaɗi ba, bayan bincike ya tabbatar da cewa ba su da hannu a aikata laifin.
Sanarwar ta ce:
"Bincike kan wannan lamari na ci gaba. Muna ƙara ƙaimi wajen gano da kuma kamo duk waɗanda suka aikata ko suka taimaka wajen aikata wannan mummunan laifi. Duk wanda aka samu da laifi za a gurfanar da shi a gaban shari'a."
Kwamishinan 'yan sandan jihar Kaduna, Muhammad Rabiu, ya sake jaddada kudirin rundunar na tabbatar da an yi wa marigayiyar adalci tare da ci gaba da tabbatar da zaman lafiya da doka a jihar.
Ya kuma buƙaci al'umma su kwantar da hankalinsu, su kasance masu bin doka, tare da ci gaba da bai wa jami'an tsaro sahihan bayanai domin taimakawa binciken.
Kisan ya jawo ce-ce-ku-ce
Kisan Malama Ummulkhairi, malamar addinin Musulunci, ya faru ne bayan wasu suka zarge ta da satar yara a Maraban Jos.
Lamarin ya jawo Allah wadai daga jami'an tsaro, ƙungiyoyin fararen hula da shugabannin al'umma, waɗanda suka bayyana abin a matsayin mummunan misali na ɗaukar doka a hannu.
Asali: Legit.ng

