Abin Tausayi: Dan Kasuwa Ya Mutu a Wani Yanayi a Dakin Fitacciyar 'Yar TikTok a Jihar Kano

Abin Tausayi: Dan Kasuwa Ya Mutu a Wani Yanayi a Dakin Fitacciyar 'Yar TikTok a Jihar Kano

  • Wani matashin ɗan kasuwa, Isma’il Makaye, ya mutu a gidan budurwarsa yar TikTok, Fati Cele da ke Danbare a jihar Kano
  • Abokan mamacin sun yi zargin cewa an ga raunuka a kansa kafin birne shi, amma dai babu wani bayani kan yanayin da ya rasu
  • Rundunar 'yan sandan Kano ta fara gudanar da bincike kan musabbabin mutuwar Isma'il Makaye yayin da ake jiran cikakken bayani

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Kano, Nigeria - Matashin ɗan kasuwa mai suna Isma’il Makaye ya mutu a wani yanayi da har yanzu ba a tantance ba a gidan budurwarsa, fitacciyar yar TikTok da aka fi sani da Fati Cele.

Rahotonnni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a gidan Fati Cele da ke a unguwar Danbare, karamar hukumar Kumbotso ta jihar Kano.

Kara karanta wannan

Dubu ta cika: An rushe katafaren gidan kasurgumin mai garkuwa da mutane da aka cafke a Edo

Isma'il.
Matashin ɗan kasuwa, Isma'il Makaye da budurwarsa yar TikTok, Fati Cele Hoto: @Northern_Trends
Source: Twitter

Daily Trust ta ruwaito cewa Isma'il Makaye, wanda ke harkar kasuwancin kayan kwalliya a yankin Hotoro Tishama, ya rasu ne a safiyar ranar Juma’a, lamarin da ya sa 'yan sanda fara bincike.

Yadda aka dauko gawar Isma'il Makaye

Wani abokin marigayin mai suna Hassan Mohammed, wanda ya ce yana cikin wadanda suka je wurin tare da jami’an ‘yan sanda, ya ce lokacin da suka isa gidan sun tarar da gawar matashin.

A cewarsa, daga bisani an kai gawar mamacin Asibitin Kwararru na Murtala Muhammad kafin a tura ta zuwa Asibitin Koyarwa na Muhammad Abdullahi Wase, inda aka tabbatar da mutuwarsa.

Ya ce:

“Mun same shi ya riga ya mutu lokacin da muka isa wurin tare da ‘yan sanda. Da farko mun je Asibitin Murtala Muhammad, daga bisani kuma aka kai shi Asibitin Abdullahi Wase inda aka tabbatar da rasuwarsa.”

Ana zargin akwai raunuka a kansa

Hassan ya kara da cewa Makaye da Fati Cele sun shafe sama da shekaru biyu suna soyayya kafin su rabu na wani lokaci bayan mamacin ya yi aure, daga bisani kuma suka sake sulhu.

Kara karanta wannan

'Yan sanda sun bindige dan ta'adda mai garkuwa da mutane

Ya bayyana cewa an samu wayoyin mamacin da kuma mukullan motarsa a wurin da lamarin ya faru, kamar yadda Leadership ta ruwaito..

Har ila yau, ya yi zargin cewa an ga raunuka a kan mamacin, yana mai cewa akwai alamun zubar jini har lokacin da aka yi masa jana’iza.

“Akwai raunuka a kansa, kuma muna zargin wata kila an bugi kansa da wani abu,” in ji shi.
Kano.
Taswirr jihar Kano da ke Arewa maso Yammacin Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

An yi jana'izar Isma'il Makaye

An yi jana’izar Isma’il Makaye a ranar Juma’a a Unguwa Uku Yan Awaki bisa koyarwar addinin Musulunci.

Fati Cele, wadda ta fito daga jihar Borno, ta shahara ne a TikTok ta hanyar bidiyoyin nishadi da raye-raye da take yi a yankin Sabon Gari da ke Kano.

Zuwa lokacin hada wannan rahoto, kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, bai amsa kiran waya da aka yi masa domin jin ta bakinsa ba.

Budurwa ta mutu a dakin saurayinta

A wani labarin, kun ji cewa wani saurayi a birnin Abuja ya shiga tashin hankali bayan mutuwar budurwarsa yayin da ta kawo masa ziyara na musamman.

Kara karanta wannan

Trump ya yi magana kan 'harin Amurka' da ya kashe yara 'yan makaranta 170 a Iran

Wani mazaunin yankin mai suna Dauda ya bayyana cewa Esther ta baro gida lafiya kalau domin ziyartar saurayinta amma aka kira yayanta aka ce masa ta mutu.

Dauda ya ce saurayin ya bayyana masa cewa ya saya wa Esther abinci lokacin da ta kawo masa ziyara, amma bayan ta ci abincin sai ta fara amai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262