An Rasa Rayuka da Wani Bam Ya Tarwatse da Motar Sulken 'Yan Sanda a Jihar Zamfara
- Jami’an rundunar ’yan sanda uku sun rasa rayukansu yayin da motarsu ta taka bam kuma ya tashi da su a jihar Zamfara
- Lamarin ya faru ne lokacin da suka fito sintiri a titin Anka zuwa Bagega kuma jami’an da suka mutu kwararru ne a fannin lalata bama-bamai
- Bayan fashewar bam din, ’yan bindiga sun kona motar sulke ta jami’an yan sandan suka fito sintiri da ita
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Zamfara, Nigeria - Jami’an rundunar ’yan sanda uku sun rasa rayukansu bayan wata motar sulke da suke ciki ta taka bam da ake zargin ’yan ta’adda sun birne a kan hanya a Jihar Zamfara.
Mai taimaka wa Gwamnan jihar Zamfara kan harkokin yada labarai, Mugira Yusuf, ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar ranar Talata.

Source: Twitter
Bam ya tashi da motar 'yan sanda
A cewar sanarwar, jami’an suna gudanar da sintiri ne a hanyar Anka zuwa Bagega domin dakile ayyukan kungiyoyin yan bindiga lokacin da hatsarin ya afku, kamar yadda Premium Times ta rahoto
Rahoton ya ce daya daga cikin motocin sulke na rundunar yan sanda ta taka wata na’urar fashewa ta IED da aka birne a kasa.
Sunayen jami’an da suka rasu
An bayyana sunayen dakarun 'yan sandan da suka mutu wanda suka hada da Sufuritanda Janar Abdulrazak Hassan, Sufeta Murtala Musa da kuma Sufeta Auwal Ahmad
Hadimin gwamnan ya ce dukkansu kwararru ne a bangaren ganowa da lalata bama-bamai (EOD) da ke aiki da rundunar ’yan sandan Jihar Zamfara.
Bayan fashewar bam din, an ce wasu ’yan bindiga sun fito daga cikin daji, inda suka banka wa motar sulken da ta lalace wuta kafin daga bisani su koma cikin daji.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a samu jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Zamfara, DSP Yazid Abubakar, kan lamarin ba.
Sabuwar dabara daga ’yan bindiga
Masana harkokin tsaro sun bayyana amfani da bama-baman da ake birnewa a hanyoyi a matsayin wata sabuwar dabara da kungiyoyin ’yan bindiga suka fara amfani da ita a Arewa maso Yamma.
A baya, galibin hare-haren ’yan bindiga a Zamfara sun fi karkata ne kan sace mutane, satar shanu da kai farmaki kan kauyuka ta amfani da bindigogi, kamar yadda Punch ta kawo.

Source: Facebook
Sai dai rahotanni sun nuna cewa yanzu wasu daga cikin wadannan kungiyoyi sun fara amfani da dabarun yaki irin na kungiyoyin Boko Haram da ISWAP da ke aiki a yankin Arewa maso Gabas.
'Yan sanda sun lalata bama-bamai
A wani rahoton, kun ji cewa rundunar ’yan sandan Zamfara ta gano wasu bama-baman da ake zargin ’yan bindiga ne suka dasa a kan titin Kunchin Kalgo.
Rahotanni sun nuna cewa jami'an tsaro sun lalata abubuwan fashewar cikin nasara ba tare da sun jawo asarar rai ko dukiya ba.
Rundunar ta tabbatar wa jama’a cewa tana ci gaba da kokarin gano tare da cafke wadanda ke da hannu wajen dasa bama-baman domin gurfanar da su a gaban kuliya.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng

