Gwamnatin Tinubu ta fara aiwatar da muhimmin aiki a Kano, zai amfani miliyoyin mutane

Gwamnatin Tinubu ta fara aiwatar da muhimmin aiki a Kano, zai amfani miliyoyin mutane

  • Hukumar FERMA ta fara gyaran titin Kano Eastern Bypass mai tsawon kilomita 13 domin rage cunkoson ababen hawa a cikin birnin Kano
  • Ana gudanar da aikin ta hanyar amfani da ma’aikatan hukumar kai tsaye tare da tura kusan ma’aikata 70 zuwa titin
  • Ana sa ran kammala aikin cikin makonni biyu bayan fara shi a ranar 23 ga Yulin shekarar 2026

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da takwas a aikin jarida

Jihar Kano - Hukumar Kula da Gyaran Hanyoyin Tarayya (FERMA) ta fara gyaran titin Kano Eastern Bypass mai tsawon kilomita 13 da ya lalace, a wani yunkuri na rage cunkoson ababen hawa a cikin birnin Kano.

Injiniyan da ke kula da aikin, Sarfil Umar, ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a lokacin duba yadda aikin ke gudana ranar Asabar, 1 ga watan Agustan 2026 a Kano.

Kara karanta wannan

Karfin hali: Yadda aka kama mutum 2 da zargin cefanar da filayen gwamnatin Kano

Za a gyara aikin titi a Kano
Taswirar jihar Kano, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Umar ya ce ana gudanar da aikin ne ta hanyar amfani da ma’aikatan hukumar kai tsaye, inda aka tura kusan ma’aikatan FERMA 70 tare da wasu ma’aikatan da aka dauka aiki zuwa sassan titin.

Ya ce titin hanya ce mai muhimmanci ta gwamnatin tarayya da ke hada hanyar Maiduguri da jihohin Katsina da Kaduna ta hanyar Kano Eastern Bypass.

Muhimmancin titin Kano Eastern Bypass

Umar ya ce gyaran titin zai taimaka wajen saukaka zirga-zirgar ababen hawa tare da kara tsawon rayuwar hanyar.

“Baya ga saukaka zirga-zirgar ababen hawa, ana sa ran aikin zai kara tsawon rayuwar titin ta hanyar hana lalacewar kwalta sakamakon ruwan sama, da rage bukatar gudanar da gyare-gyare masu tsada a gaba."
“Haka kuma, aikin zai rage kudin tafiyar da ababen hawa ga dubban matafiya da masu safarar kaya da ke amfani da hanyar a kullum."
“Titin na da matukar muhimmanci wajen zirga-zirga a Kano, domin yana hada motocin da ke tafiya mai nisa daga Arewa maso Gabas zuwa Arewa maso Yamma, tare da bai wa masu ababen hawa damar kauce wa cunkoson da ake samu a cikin birnin.” In ji shi

Kara karanta wannan

Yadda aka ware N400bn na gyaran masallatai, masarautu a kasafin kudin 2026

Ya bayyana cewa manyan motoci masu dauke da amfanin gona, dabbobi, man fetur da kayayyakin masana’antu suna yawan amfani da titin wajen safarar kaya tsakanin Kano da jihohin da ke makwabtaka da ita.

Saboda haka, ya ce yanayin titin na da matukar muhimmanci ga harkokin kasuwanci da safarar kaya a yankin.

Lokacin kammala aikin

Umar ya ce an fara aikin gyaran ne a ranar 23 ga Yuli, kuma ana sa ran kammala shi cikin makonni biyu.

A cewarsa, aikin ya hada da toshe ramukan da ke kan titi, cire laka daga magudanan ruwa, kwashe shara da sauran abubuwan da suka toshe hanyoyin ruwa, da kuma gyara ginshikan fitilun titin da suka lalace a kan hanyar mai bangarori biyu.

Ya ce an ga bukatar gudanar da aikin ne sakamakon daminar da ake ciki, yana mai bayyana cewa toshewar magudanan ruwa na sa ruwa ya dade a kan tituna, wanda yana daga cikin manyan abubuwan da ke haddasa lalacewar hanyoyin tarayya.

Barazanar ruwa ga tituna

Umar ya ce kula da magudanan ruwa na daga cikin muhimman hanyoyin kare tituna, domin tsayuwar ruwa na raunana tubalin titin, da kara yawan ramuka, tare da rage tsawon rayuwar kwalta.

Kara karanta wannan

Shiri ya kankama: Tinubu zai yi wani babban aiki na Naira tiriliyan 1.05 a Kano

Ya bukaci mazauna yankin da masu amfani da titin su daina zuba shara a magudanan ruwa. Umar ya gargadi cewa toshewar hanyoyin ruwa na kara hadarin ambaliya tare da jefa jarin da gwamnati ta zuba wajen gina hanyoyi cikin hadari.

Gwamnatin Tinubu za ta gyara titi a Kano
Shugaban kasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu Hoto: @aonanuga1956
Source: Twitter

Gwamnatin Kano za ta gina titi

A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya ce ya kaddamar da fara gina titin karkara mai nisan kilomita 7.2 daga Mil Goma zuwa 'Yankatsari.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ce gwamnatin Kano za ta kashe Naira biliyan 2.6 wajen aiwatar da aikin gina titin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com