Mutuwa Ta Girgiza Sarakunan Najeriya, Osi Balogun Ya Riga Mu Gidan Gaskiya a Ibadan
- Osi Balogun na masarautar Ibadanland da ke jihar Oyo, Oba Olubunmi Isioye-Dada, ya rasu bayan gajeruwar rashin lafiya
- Rahotanni daga wasu majiyoyi sun nuna cewa basaraken ya rasu a gidansa da ke Ibadan, babban birnin jihar Oyo da ke Kudancin Najeriya
- Rasuwarsa ta haifar da gurbi a tsarin sarautar Ibadan wanda zai jawo karin girma ga wasu hakimai da sarakuna
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Ibadan, Nigeria - Al’ummar jihar Oyo sun shiga alhini bayan rasuwar Osi Balogun na Ibadanland, Oba Olubunmi Isioye-Dada, wanda ya rasu bayan fama da gajeruwar rashin lafiya.
Wata majiya daga cikin masu fada a ji a fadar Ibadanlamd da ta nemi a sakaya sunanta, ta tabbatar da rasuwar basaraken a wata tattaunawa ta wayar tarho.

Source: Facebook
Basarake ya rasu a birnin Ibadan
Majiyar ta shaida wa jaridar Tribune Nigeria cewa Oba Isioye-Dada ya rasu ne a gidansa da ke Ibadan bayan ya yi fama da rashin lafiya na dan wani lokaci.
Majiyar ta kara da cewa jim kadan bayan samun labarin rasuwar, tawagar Omo Oye ta tafi gidan marigayin domin gudanar da al’amuran da suka dace da kuma nuna alhini ga iyalansa da masoyansa.
Wane ne Oba Isioye-Dada?
Kafin rasuwarsa, Oba Olubunmi Isioye-Dada ya kasance Osi Balogun na Ibadanland, daya daga cikin manyan mukaman gargajiya a tsarin sarautar Ibadan.
An san shi da taka muhimmiyar rawa wajen kula da al’amuran gargajiya da ci gaban masarautar Ibadan, tare da ba da gudunmawa wajen tabbatar da zaman lafiya da hadin kai tsakanin al’umma.
Rasuwar za ta sauya tsarin mukamai
Rasuwar Osi Balogun ta bude gurbi a jerin mukaman masarautar Ibadan, lamarin da zai haifar da karin girma ga wasu hakimai da sarakuna a bangaren Balogun.
Bisa tsarin sarautar Ibadan, idan wani babban hakimi ya rasu ko ya bar mukami, wadanda ke kasa da shi sukan samu karin matsayi domin cike guraben da aka samu.
Bayan amincewar Olubadan na Ibadanland, Oba Rashidi Ladoja, Sanata Sharafadeen Ali, wanda ke rike da mukamin Ekaarun Balogun, zai samu karin girma zuwa Ekerin Balogun na Ibadanland.
Haka kuma, Oba Akeem Mobolaji Adewoyin zai tashi daga mukamin Ekerin Balogun zuwa Asipa Balogun na Ibadanland, kamar yadda Daily Post ta rahoto.
Masu bibiyar harkokin sarauta a Ibadan sun bayyana cewa wadannan sauye-sauye na daga cikin tsarin gargajiya da ake bi wajen tabbatar da dorewar shugabanci a masarautar.

Source: Original
Ana jiran sanarwar masarauta
A halin yanzu, jama'a da masoya marigayin na ci gaba da aika sakonnin ta'aziyya ga iyalansa da masarautar Ibadanland.
Ana sa ran fadar Olubadan za ta fitar da cikakken bayani kan jana'izar marigayin da kuma matakan da za a dauka game da sauye-sauyen mukaman sarautar da rasuwarsa ta haifar.
Sarkin Gazargamu ya kwanta dama
A wani labarin, kun ji cewa Sarkin Gazargamu na jihar Yobe, Mai Martaba Alhaji Ahmad Tijjani Ibn Saleh, ya rasu bayan ya shafe lokaci yana fama da rashin lafiya.
Rahotanni sun nuna cewa sarkin ya rasu ne a ranar Talata, 9 ga watan Yuni, 2026 a birnin Alkahira na ƙasar Masar.
An bayyana marigayin a matsayin uba, jagora kuma sarki wanda ya sadaukar da rayuwarsa wajen yi wa al’ummarsa da bil’adama hidima.
Asali: Legit.ng

