Janar Abdulsalam Ya Faɗi Abin da ba a Sani ba kan Mutuwar Fuju'a da Abiola Ya Yi

Janar Abdulsalam Ya Faɗi Abin da ba a Sani ba kan Mutuwar Fuju'a da Abiola Ya Yi

  • Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya ya kawo wasu karin bayanai game da mutuwar MKO Abiola a Najeriya
  • Abdulsalam ya ce ba a ba tawagar Amurka damar ganin Abiola ba da farko, amma ya ba da umarnin a kai su wajensa
  • Ya bayyana cewa Abiola ya fara tari da zufa yayin ganawa da tawagar kafin daga bisani ya rasu, lamarin da ya girgiza kasar

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Minna, Niger - Janar Abdulsalami Abubakar mai ritaya ya bayyana a cikin tarihin rayuwarsa kan mutuwar MKO Abiola.

Tsohon shugaban kasar ya bayyana cewa jami'an Amurka da suka zo Najeriya domin ganawa da MKO Abiola an hana su ganinsa da farko.

Janar Abdulsalam ya yi magana kan mutuwar Abiola
Marigayi tsohon ɗan takarar shugaban kasa a Najeriya, Mashood Abiola. Hoto: historylovers_001, PIERRE BOUSSEL.
Source: Getty Images

Musabbabin mutuwar MKO Abiola

A cewar bayanan da aka bayar, Abiola ya fara tari ba tsammani sannan daga baya ya rasu, lamarin da ya jawo tarzoma a Lagos, cewar TheCable.

Kara karanta wannan

"Suna tare cikin daki"; Tsohon jami'in DSS ya fadi abin da ya kashe Janar Sani Abacha

Abiola, wanda ya lashe zaben shugaban kasa na ranar 12 ga Yunin 1993 da aka soke, ya gana da wata tawagar mutanen Amurka a Abuja ranar 7 ga Yulin 1998.

An yi ta rade-radin cewa an ba shi shayin da ya kunshi guba daga jami'an Amurka domin rage tari da ya fara yi.

Wata guda kafin haka ne Janar Sani Abacha ya rasu babu zato babu tsammai, bayan ya tsare Abiola tun shekarar 1994.

Abdulsalami ya ce tawagar Amurka ta zo Najeriya domin tantance yanayin siyasar kasar bayan mutuwar Abacha da kuma tattaunawa da masu ruwa da tsaki.

Janar Abdulsalam ya tuna yadda Abiola ya mutu a Najeriya
Tsohon shugaban kasa a mulkin soja, Abdulsalam Abubakar. Hoto: Anadolu Ajansi.
Source: Getty Images

Yadda aka hana su Abdulsalam ganin Abiola

A cewar Abdulsalami, sun koka cewa an hana su ganin Abiola duk da cewa wannan ne babban dalilin zuwansu Najeriya.

Ya ce ya yi mamakin hakan domin bai san an hana su ba, inda nan take ya umarci CSO dinsa Abdulrasheed Aliyu ya shirya ganawar.

Bayan kiran waya daga Aliyu, Abdulsalami ya samu labarin cewa Abiola ya mutu bayan ya fara tari da zufa a wajen taron, cewar The Nation.

Kara karanta wannan

'Sai dai Trump ya mika wuya': Dan majalisa a Iran game da yaki da Amurka

Abdulsalami ya ce sanar da iyalan Abiola labarin mutuwarsa abu ne mai matukar wahala, inda daya daga cikin 'ya'yansa ta fashe da kuka.

Binciken da aka yi kan mutuwar Abiola

An tattaro kwararrun likitocin binciken gawa daga Amurka, Birtaniya, Najeriya da Canada domin gudanar da binciken cikin gaskiya.

Dr Falomo da wakilan 'Nigerian Medical Association' sun halarci dukkan matakan binciken ba tare da wani boye-boye ba.

Rahoton ya nuna cewa Abiola na fama da matsananciyar cutar zuciya ta dogon lokaci da kuma hawan jini.

An gano jijiyoyin zuciyarsa sun toshe sakamakon taruwar kitse, yayin da zuciyarsa ta kara girma saboda hawan jini.

Sakamakon binciken sinadaran jiki bai nuna wata alamar guba ba, lamarin da ya kawar da zarge-zargen kisa.

Wani likitan Amurka, Dr John Pless, ya ce cutar da ta yi sanadin mutuwar Abiola ta dade a jikinsa tsawon shekaru 10 zuwa 14.

Abdulsalam ya magantu kan dawowar mulkin soja

Mun ba ku labarin cewa tsohon shugaban Najeriya Janar Abdulsalami Abubakar ya yi magana kan masu neman mulkin soja a Najeriya maimakon dimokuraɗiyya.

Kara karanta wannan

Sheikh Bala Lau ya yi magana kan shugaban Izala da ya mutu a hannun 'yan bindiga

Janar Abdulsalami Abubakar ya yi magana ne bayan Najeriya ta kwashe shekaru 25 tana mulkin farar hula duk da ƙalubalen da kasar ke fuskanta.

A daya bangaren, Shugaban majalisar dokokin Najeriya ya ce ƙarfafa jam’iyyun siyasa da adawa mai ma'ana na samar da shugabanci nagari.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.