Majalisar Dattawa Ta Kunyata Sanata kan Umarnin Kama Tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kyari

Majalisar Dattawa Ta Kunyata Sanata kan Umarnin Kama Tsohon Shugaban NNPCL, Mele Kyari

  • Majalisar Dattawa ta musanta ba da sammacin kama tsohon shugaban kamfanin mai na Najeriya, NNPCL, Mele Kyari
  • Sanatoci sun bayyana cewa shugaban majalisa ne kaɗai ke da iko da karfin fitar da irin wannan sammaci a hukumance
  • Majalisar ta ce kwamitin kula da asusun gwamnatin Najeriya ya wuce iyakarsa, ta kuma nesanta kanta da kalaman Adams Oshiomhole

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Majalisar Dattawa ta ce ba ta amince da sammacin kama tsohon Shugaban Kamfanin Man Fetur na Kasa (NNPCL), Mele Kyari, wanda Kwamitin Kula da Asusun gwamnati ya fitar ba.

Lamarin ya taso ne a zaman majalisar na yau Alhamis, bayan shugaban masu rinjaye, Sanata Opeyemi Bamidele, ya gabatar da batun karkashin dokokin majalisa.

Majalisa.
Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio na jagorantar zaman Majalisa a Abuja Hoto: @NGRSenate
Source: Facebook

Majalisa ta soke sammacin kama Mele Kyari

A rahoton The Cable, Bamidele jaddada cewa doka ta bai wa shugaban majalisar dattawa kaɗai ikon fitar da sammaci domin tilasta wa wani shaida halartar zaman majalisa ko na kwamitocinta.

Kara karanta wannan

NNPCL: Mele Kyari ya aiko sako daga kasar waje bayan ba da umarnin kama shi

Bayan tattaunawa, sanatocin sun yanke shawarar cewa sammacin da kwamitin ya fitar bai dace da doka ba saboda kwamitin ya wuce gona da iri.

Majalisar ta kuma umurci dukkan kwamitocinta da su bi kundin tsarin mulki, dokokin majalisa da ka'idojin aikinsu yayin gudanar da bincike da sa ido.

Majalisar dattawa ta yi fatali da kalaman Oshiomhole

Majalisar ta kuma bayyana cewa kalaman da aka danganta wa Sanata Adams Oshiomhole na cewa NNPCL "gungu ne na barayi da masu laifi" ba daga gare ta suka fito ba.

Sanatoci sun ce dole ne a mutunta ka'idar sauraron ɓangarorin biyu, adalci da kuma rashin yanke hukunci kafin kotu ta yanke.

Barau da wasu sanatoci sun yi martani

Mataimakin shugaban majalisar dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya ce kwamitin ya yi kuskure a matakin da ya dauka kan Mele Kyari.

"Fitar da sammaci aiki ne na shugaban majalisa. Kwamitin ya wuce iyakarsa," in ji Barau.

Shi ma babban mai tsawatarwa na majalisa, Sanata Tahir Monguno, ya ce dole ne majalisa ta kasance abin koyi wajen bin doka.

Kara karanta wannan

Bidiyo: Mimbarin siyasa ya ruguzo kasa gwamna na tsaka da bayani a kamfe

Sanata Orji Uzor Kalu da Sanata Adamu Aliero sun bukaci Oshiomhole ya janye kalamansa kan NNPCL.

Sanata Oshiomhole ya kare kansa

Da aka ba shi damar magana, Oshiomhole ya ce furucin nasa ya fito ne bayan wani tsohon jami'in kudi na NNPCL ya yi kalaman da ya dauka a matsayin cin zarafin sanatoci.

Ya amince cewa ya yi magana cikin fushi, amma ya ce manufarsa ita ce kare martabar majalisar dattawa, kamar yadda The Nation ta rahoto.

Adams.
Sanata Adams Oshiomhole a zaman Majalisar dattawa Hoto: Adams Oshiomhole
Source: Facebook

Tsohon gwamnan ya ce:

"Na yi magana ne cikin fushi, amma akwai masu gudanarwa nagari da yawa a NNPCL."

Ya kara da cewa bai yi niyyar bata sunan dukkan ma'aikatan kamfanin ba, sai dai ya mayar da martani ne ga abin da ya faru a zaman kwamitin.

Mele Kyari ya maida martani

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon shugaban kamfanin mai na kasa (NNPCL), Malam Mele Kyari, ya ce ya yi mamakin sammacin kama shi da kwamitin Majalisar Dattawa ya fitar.

Ya musanta zargin cewa ya yi biris da gayyatar Majalisar Dattawa, inda ya ce bai ga wata sabuwar gayyata daga kwamitin ba kafin a bada sammacin kama shi.

Malam Mele Kyari ya bayyana cewa yanayin lafiyarsa a halin yanzu ne ya hana shi damar halartar zaman kwamitin kai tsaye.

Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262