Fatima Ta Yi Nasara, Kotu Ta Yanke Hukunci kan Hausawan da Aka Haifa a Jos ta Arewa

Fatima Ta Yi Nasara, Kotu Ta Yanke Hukunci kan Hausawan da Aka Haifa a Jos ta Arewa

  • Babbar Kotun Jihar Filato ta yanke hukuncin cewa duk wani Bahaushe da aka haifa kuma ya taso a Jos ta Arewa ɗan asalin yankin ne
  • Kotu ta umarci ƙaramar hukumar Jos ta Arewa ta ba Fatima Baba Akawu takardar shaidar zama cikakkiyar 'yan asalin ƙasa
  • Alƙalin kotun, Mai shari'a C. Donglong ya ce nuna bambanci saboda ƙabila ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Najeriya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Jos, Nigeria - Babbar Kotun Jihar Filato mai lamba 17 ta yanke hukuncin cewa Hausawan da aka haifa kuma suka taso a ƙaramar hukumar Jos ta Arewa 'yan asalin yankin ne.

Mai shari'a C. Donglong ne ya yanke hukuncin a ƙarar da Fatima Baba Akawu da mahaifinta, Baba Alhaji Akawu, suka shigar kan ƙin ba ta takardar shaidar yar asalin ƙasa daga ƙaramar hukuma.

Kara karanta wannan

NDC ta ce an samu kura kurai a zaben fitar da gwani, ta nemi afuwa

Kotu.
Gudumar da alkalai ke amfani da ita a kotunan Najeriya Hoto: Anadolu
Source: Getty Images

Dalilin shigar da ƙara a kotu

Daily Trust ta ce masu ƙarar sun nemi kotu ta fayyace ko Fatima Baba Akawu, wadda aka haifa a Jos ta Arewa kuma mahaifinta ɗan asalin yankin ne, tana da damar samun takardar shaida duk da kasancewarta Bahaushiya.

Sun kuma kalubalanci matakin ƙaramar hukumar na ba ta takardar zama maimakon takardar yar asalin yankin, yayin da aka ba wani mutum mai suna Dung Bot, ɗan ƙabilar Berom, takardar ɗan asalin ƙasa a rana guda.

Alƙali ya soki nuna bambanci

Da yake yanke hukunci, Mai shari'a Donglong ya amince da dukkan buƙatun masu ƙarar.

Ya bayyana cewa matakin da ƙaramar hukumar ta ɗauka na ba Fatima takardar zama saboda asalinta na Bahaushiya, amma ta ba wani ɗan Berom takardar ɗan asali, wani nau'i ne na nuna bambanci da ya saɓa wa kundin tsarin mulkin Najeriya.

Alƙalin ya jaddada cewa kotu tana da alhakin kare haƙƙin kowane ɗan Najeriya daga wariya bisa ƙabila ko asalinsa.

Kara karanta wannan

Sace dalibai: Gwamna ya umarci rufe makarantu bayan samun rahoton DSS

Umarnin da kotu ta bayar

Kotu ta ayyana cewa saboda Baba Alhaji Akawu cikakken ɗan asalin Jos ta Arewa ne, dukkan 'ya'yansa da aka haifa kuma suka taso a yankin, ciki har da Fatima, suna da cikakkiyar damar a gane su a matsayin 'yan asalin karamar hukumar.

Filato.
Taswirar jihar Filato da ke Arewa ta Tsakiya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Har ila yau, kotun ta bayar da umarnin da ya hana ƙaramar hukumar Jos ta Arewa ci gaba da ba mutane takardar zama a matsayin madadin takardar ɗan asalin ƙasa.

Alƙalin ya bayyana cewa irin wannan takarda ba ta da tushe a doka kuma ba za ta iya maye gurbin takardar ɗan asalin ƙasa ba.

Kotu ta tura Halima Umar gidan yari

A wani labarin, kun ji cewa kotu ta yanke wa wata mata, Halima Umar hukuncin daurin shekaru 20 a gidan gyaran hali bisa mallakar tarin makamai ba bisa ka'ida ba.

Rahotanni sun nuna cewa an kama matar da laifin mallakar harsasai 302 na bindigar AK-47 ba bisa ka’ida ba da yunkurin bayar da tallafi wajen aikata ayyukan ta’addanci.

Hukumar tsaro ta DSS ta gurfanar da Halima Umar a gaban kotu ne a ranar 11 ga Maris, 2026 bayan kama ta da makamai da ake zargin za ta kai wa 'yan bindiga a jihar Filato.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262