Kotu Ta Yanke wa Halima Umar Hukunci bayan Kama Ta da Makamai Masu Hadari a Filato
- Kotu ta yanke wa wata mata, Halima Umar hukuncin daurin shekaru 20 a gidan gyaran hali bisa mallakar tarin makamai ba bisa ka'ida ba
- Matar dai ba ta wahal ta kotu ba, ta amsa wasu daga cikin laifuffukan da ake tuhumarta da su tun a ranar da DSS ta gurfanar da ita
- Hukumar DSS ta kama Halima ne a jihar Filato dauke da harsasai 302 na bindigun AK-47, wanda ake zargin za ta sayar wa yan ta'adda
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja karkashin Mai Shari’a Hauwa Yilwa ta kama wata mata, Halima Haliru Umar da laifin mallakar makamai masu hadari ba bisa ka'ida ba.
Kotun ta yanke wa matar hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari bayan samunta da laifin mallakar harsasai 302 na bindigar AK-47 ba bisa ka’ida ba da yunkurin bayar da tallafi wajen aikata ayyukan ta’addanci.

Source: Getty Images
Wacce aka yankewa hukuncin ta amsa laifuffuka biyu daga cikin tuhume-tuhume hudu da Hukumar Tsaro ta DSS ta shigar a kanta, kamar yadda Channels tv ta ruwaito.
DSS ta cafke Halima a Filato
Tun farko dai hukumar tsaro ta DSS ta gurfanar da Halima Umar a gaban kotu ne a ranar 11 ga Maris, 2026 bayan kama ta da makamai da ake zargin za ta kai wa 'yan bindiga a jihar Filato.
Bayan gurfanar da ita, an sake duba bayanan laifuffukan da ke cikin tuhuma ta uku da ta hudu wadanda ta amsa laifinsu ba tare da bata lokaci ba.
Yadda Halima ta amsa laifuffuka a kotu
A hukuncin da ta yanke yau Juma'a, Mai Shari’a Yilwa ta bayyana cewa wacce ake tuhuma ta amsa laifuffukan da ke cikin tuhume-tuhume na uku da na hudu tun ranar da aka gurfanar da ita.
Ta kara da cewa bisa amincewar da ta yi da laifin, ta karbi dukkan bayanan da masu gabatar da kara suka gabatar ba tare da kawo wata hujja domin kare kanta ba.

Kara karanta wannan
Malami ya yi abin kunya, kotu ta kama shi da laifin dirka wa 'yan mata ciki a Kwara
Lauya ya nema wa matar sassauci
Bayan an same ta da laifi, lauyanta Hamza Dantani ya roki kotu ta sassauta hukuncin da za ta yanke mata, cewar rahoton da Zagazola Makama ya wallafa a X
Dantani ya ce Halima ba ta taba aikata wani laifi a baya ba kuma tana nadamar abin da ta aikata, kuma ba ta bata wa kotu lokaci ba dangane da zargin da ake mata.
Lauyan ya bayyana wa kotu cewa wacce ake tuhuma uwa ce mai shayarwa wadda aka kama tare da jaririnta mai shekara guda, yana rokon kotu ta hada adalci da jin kai.

Source: Twitter
Hukuncin da kotu ta yanke
Lauyan masu gabatar da kara, Caliistus Eze, ya shaida wa kotu cewa babu wani bayani da ke nuna cewa an taba hukunta Halima a baya.
Mai Shari’a Yilwa, wadda ta dakatar da zaman kotun na dan lokaci, daga baya ta dawo ta yanke mata hukuncin daurin shekaru 20 kan tuhumq uku, sannan shekara guda kan tuhuma ta hudu.
An gurfanar da mutane 20 kan ta'addanci
A wani labarin, kun ji cewa gwamnatin tarayya karkashin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ta dawo da shari'o'in wadanda ake zargi da hannu a ayyukan ta'addanci a Najeriya.
Rahoto ya nuna cewa gwamnatin ta gurfanar da akalla mutane 20 da ake zargi da ta'addanci a gaban babbar kotun mai zama a Abuja.
Bayanai sun nuna cewa an girke jami'an tsaro a muhimman wurare da titunan zuwa kotun domin tabbatar da tsaro a lokacin shari'ar wadanda ake zargin.
Asali: Legit.ng

