Kotu Ta Taka wa Majalisar Tarayya Birki kan Shirin Sayan Motocin Alfarma na N110bn
- Babbar Kotun Tarayya da ke Lagos ta soke shirin kashe N110 biliyan na Majalisar Tarayya kan motocin SUV da alawus
- Kotun ta ce kashe N40 biliyan da N70 biliyan ga ‘yan majalisa ya saba ka’ida, yana nuna cin moriyar kai da rashin bin gaskiya
- SERAP ta yabawa hukuncin kotu, yayin da aka umarci Godswill Akpabio da Tajudeen Abbas su tabbatar duk kudaden gwamnati kashe su bisa doka
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Abuja - Babbar Kotun Tarayya da ke zaune a Lagos ta yi hukunci kan shirin kashe makudan kudi na biliyoyin Naira
Majiyoyi suka ce Majalisar Tarayya na shirin kashe makudan kudin wanda kotun ta bayyana a matsayin haramun da saba dokoki

Source: Twitter
Kotun ta kuma bayyana cewa kashe N40 biliyan wajen sayen motocin ‘yan majalisa 465 da kuma N70 biliyan a matsayin saba doka, cewar Punch.
Hukuncin ya kuma umarci Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, da Kakakin Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas, su tabbatar cewa duk kashe kudaden gwamnati a gaba na Majalisa zai bi doka, gaskiya da rikon amana.
An yanke hukuncin ne ranar Laraba, 6 ga Mayu, 2026, a cikin shari’a mai lamba FHC/L/CS/1606/2023 wadda ƙungiyar SERAP ta shigar a kan Majalisar Tarayya.
Kwafin hukuncin da aka tabbatar ya bayyana a ranar Lahadi, inda SERAP ta ce ta shigar da karar ne tun watan Agusta 2023 saboda shirin kashe kudin a lokacin da ake fama da matsin tattalin arziki a ƙasar.
Alkalin kotu, Mai Shari’a Yellim Bogoro, ta ce irin wannan kashe kudi ba tare da bin ka’ida ba yana nuna rashin gaskiya da amfani da ofis don cin moriyar kai.
Ta ce:
“Girman kudin da aka kashe da rashin bin ka’ida ya nuna cewa aikin ya saba doka kuma ba shi da adalci.”
Ta kuma kara da cewa masu amfana da kudin su ne wadanda suke amincewa da shi, abin da ke nuna cin moriyar kai da rikicin anfani.
Kotun ta ce a halin da Najeriya ke ciki na matsin tattalin arziki, irin wannan kashe kudi ba ya fifita bukatun kasa.

Kara karanta wannan
Jerin matan Arewa 4 da jam'iyyar APC ta tsaida takarar Majalisar wakilai a zaben 2027
Ta kuma ce kariyar “ikon majalisa” ba za ta zama kariya ga karya doka ba, domin kotu na da ikon sa ido kan bin doka da kundin tsarin mulki.
SERAP ta ce hukuncin babban nasara ne ga gaskiya, rikon amana da ingantaccen amfani da kudin jama’a a Najeriya.
Lauyan kare hakkin dan adam, Femi Falana (SAN), ya ce dole ne a yaba da hukuncin, yana mai cewa rayuwar ‘yan kasa a halin matsin tattalin arziki ba za a yi watsi da ita ba saboda jin daɗin ‘yan siyasa.
Kotun ta tabbatar cewa wannan kashe kudi ya saba dokar sayen kaya ta Public Procurement Act, ka’idojin aikin gwamnati da rantsuwar ofis na kundin tsarin mulki.
An kuma umarci a ci gaba da bin doka da gaskiya a duk wani kashe kudin gwamnati a gaba, domin kauce wa cin zarafin dukiyar kasa.
Ƙarin bayani na tafe ....
Asali: Legit.ng
