Atiku Abubakar Ya Dauki Zafi, Ya Maida Martani kan Kalaman Babachir Lawal

Atiku Abubakar Ya Dauki Zafi, Ya Maida Martani kan Kalaman Babachir Lawal

  • Dan takarar shugaban kasa na ADC, Atiku Abubakar ya nuna damuwa game da kalaman tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir lawal
  • Atiku y ce Babachir na neman haddasa rabuwar kai tsakanin 'yan Najeriya, yana mai cewa bai kamata ya nun kabilanci ba
  • Tsohon mataimakin shugaban kasar ya musanta zargin cewa bai nuna damuwa ga wadanda hare-hare da tashe-tashen hankula suka shafa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya maida martani ga kalaman tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya (SGF), Babachir David Lawal.

Atiku ya zargi Babachir da yin kalamai da ka iya rusa hadin kan da ke tsakanin 'yan Najeriya da kuma nuna bambancin kabila.

Atiku.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar yana magana a wurin taro Hoto: Atiku Abubakar
Source: Facebook

Atiku ya caccaki Babachir Lawal

Daily Trust ta ce martanin tsohon mataimakin shugaban kasar na kunshe a wata sanarwa da mai taimaka masa na musamman kan hulda da jama'a, Phrank Shaibu, ya fitar ranar Lahadi

Kara karanta wannan

Babachir ya fadi wanda ya yi kulle kulle aka kore shi a gwamnatin Buhari

Atiku ya ce abin takaici ne yadda Babachir ya zabi yin zarge-zarge da hasashe ba tare da gabatar da hujjojin da za su gaskata maganganunsa ba.

'Dan takarar shugaban kasa na ADC ya ce duk da dogon bayani da zarge-zargen da Babachir ya yi a kansa, bai gabatar da wata hujja da za ta tabbatar da zarge-zargen da yake yi ba.

Atiku ya yi fatali da dorawa kabila laifi

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana cewa abin da ya fi damunsa shi ne yadda Babachir ke kokarin alakanta wata kabila baki daya da aikata laifuffuka.

Ya ce abu ne mai hatsari da rashin adalci a dora wa wata kabila laifin wasu mutane saboda kawai suna da asali daya.

A cewarsa, idan aka bi irin wannan tunanin, za a iya dora wa kowace kabila laifukan da wasu tsiraru daga cikinta suka aikata, lamarin da zai iya haifar da rabuwar kai a kasa.

Abin da ya ba Atiku Abubakar mamaki

Atiku ya ce abin mamaki ne yadda Babachir ke sukar kabilar da tsohon shugaban kasa Muhammadu Buhari ya fito daga cikinta.

Kara karanta wannan

Gwamnatin Katsina ta yi magana kan sace Janar da matarsa, ta fadi kokarin da take yi

Ya tuna cewa Buhari ne ya nada Babachir a matsayin Sakataren Gwamnatin Tarayya, mafi girman mukamin da ya taba rike wa a gwamnati.

Ya ce:

"Babachir bai ki karbar mukami ko damar da ya samu daga shugaba Bahaushe-Fulani ba.
"Don haka yana da wahala a fahimci dalilin da ya sa yanzu yake kokarin bata sunan wata kabila saboda wani dan cikinta yana neman shugabancin kasa ta hanyar dimokuradiyya."
Babachir.
Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David lawal Hoto: Babachir Lawal
Source: Facebook

Yadda Atiku ya kare kansa daga zargi

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya musanta zargin cewa bai nuna damuwa ga wadanda hare-hare da tashe-tashen hankula suka shafa ba, kamar yadda Punch ta kawo.

Ya ce tsawon shekaru yana ci gaba da yin Allah-wadai da ta'addanci, garkuwa da mutane, rikice-rikicen kabilanci da addini da sauran matsalolin tsaro a Najeriya.

Atiku ya soki Tinubu kan matsalar tsaro

A wani rahoton, kun ji cewa tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki yadda gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ke tafiyar da sha'anin tsaro.

Atiku ya jaddada cewa tsarin tsaron ƙasar yana buƙatar sauyi cikin gaggawa domin magance barazanar tsaro da ke ƙara yaduwa a Najeriya.

Ya buƙaci gwamnatin tarayya da ta hanzarta gudanar da cikakkiyar bita kan tsarin manufofin yaƙi da ta'addanci na Najeriya.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262