Akwai Matsala: Abubuwa 4 da 'Yan Ta'adda Suka Nema kafin Su Sako Dalibai da Malaman Oyo

Akwai Matsala: Abubuwa 4 da 'Yan Ta'adda Suka Nema kafin Su Sako Dalibai da Malaman Oyo

  • 'Yan bindigar da suka sace dalibai a makarantu uku a jihar Oyo sun gindaya sharudda hudu kafin sako duka mutanen da ke hannunsu
  • Daga cikin sharuddan da aka ce sun kafa har da sakin wasu manyan jagororin kungiyar Ansaru da ke tsare a hannun jami'an tsaro
  • Gwamnatin Oyo ta ki cewa komai kan abubuwan da masu garkuwar suka nema, ta ce fadin halin da ake ciki zai iya kawo cikas

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Oyo, Nigeria - Rahotanni sun nuna cewa ‘yan ta’adda da ke rike da malamai da daliban da aka sace daga makarantu uku a karamar hukumar Oriire ta jihar Oyo sun gabatar da sharuɗɗa guda huɗu.

An kai farmaki a makarantu da ke Esinele, Yawota da Alawusa a ranar 15 ga watan Mayu, inda aka sace dalibai da malamai da dama.

Kara karanta wannan

Satar dalibai: Hanyoyi 6 da makarantu za su bi su kare kansu daga 'yan bindiga a Najeriya

Jihar Oyo.
Taswirar jihar Oyo da ke yankin Kudu maso Yamma Hoto: Legit.ng
Source: Original

Abubuwa 4 da masu garkuwa suka nema

Jaridar Punch ta tattaro cewa masu garkuwar sun ce dole ne a cika wasu bukatu kafin su saki wadanda ke hannunsu.

Daga cikin sharuddan da yan ta'addan suka kafa har da sakin wasu shugabanninsu da ake tsare da su, biyan kudin fansa, samar da motoci kirar Hilux guda biyu, da kuma aiwatar da dokokin Shari’a a wasu fannoni.

'Yan ta'adda sun nemi sakin shugabannin Ansaru

Rahotanni sun ce daga cikin wadanda ake neman a sako akwai Mahmud Usman (wanda aka fi sani da Abu Bara’a ko Abbas Mukhtar) da mataimakinsa Abubakar Abba (wanda aka fi sani da Isah Adam ko Mahmud Al-Nigeri).

Wadannan mutanen su ne shugabannin kungiyar Jama’atu Ansarul Muslimeena Fii Bilaadis Sudan (JAMBS), wacce aka fi sani da Ansaru, wata kungiyar da ta balle daga Boko Haram.

An zarge su da hannu a ayyukan ta’addanci tsakanin shekarar 2013 zuwa 2015, tare da alakanta su da fashin gidan yarin Kuje da aka yi a 2022.

Kara karanta wannan

Majalisar dinkin duniya ta turo sako kan daliban da aka sace a jihohin Borno da Oyo

Yadda aka gurfanar da jagororin Ansarun

Rahotanni sun ce an kama su tsakanin watan Mayu zuwa Yuli 2025, kuma suna fuskantar shari’a a babbar kotun tarayya da ke Abuja.

Mahmud Usman ya amsa laifi daya na hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, inda ya bayyana cewa yana amfani da kudin wajen sayen makamai da daukar nauyin ayyukan garkuwa da mutane.

Sai dai ya musanta wasu tuhume-tuhume 31 da ake yi masa, yayin da yake tsare a hannun DSS, kamar yadda Vangaurd ta ruwaito.

Shi ma mataimakinsa, Abba, ya musanta dukkan tuhume-tuhume 32 da ake masa, kuma shari’arsa na ci gaba a kotu.

Gwamna Makinde.
Gwamnan jihar Oyo, Seyi Makinde yana magana a taron kwamishinoni a Ibadan Hoto: Seyi Makinde
Source: Facebook

Matsayar gwamnatin jihar Oyo

Rahotanni sun ce masu garkuwar na neman kudin fansa har Naira biliyan daya (₦1bn), wanda za a tura zuwa asusun banki a Jamhuriyar Benin, duk da cewa ba a tabbatar da sahihancin wannan adadi ba.

Gwamnatin Oyo ta ce ba za ta yi tsokaci kan sharuɗɗan ko yadda ake tattaunawa ba, Kwamishinan Yada Labarai, Dotun Oyelade, ya ce bayyana dabarun gwamnati zai iya kawo cikas ga kokarin ceto wadanda aka sace.

Kara karanta wannan

'Yan bindiga sun shiga Abuja da sassafe, sun kashe mutane sun dauke wasu

'Yan bindiga sun sako daliban Oyo?

A baya, kun ji cewa Gwamnatin jihar Oyo ta musanta wani bidiyo da ke yawo a kafafen sada zumunta wanda ke ikirarin cewa dalibai da malami da aka sace sun kubuta.

A cikin wata sanarwa, Kwamishinan Yada Labarai da Wayar da Kan Jama'a na jihar, Prince Dotun Oyelade, ya bayyana cewa rahoton ba gaskiya ba ne.

Oyelade ya jaddada cewa sabanin abin da ake yadawa a shafukan sada zumunta, har yanzu wadanda aka yi garkuwa da su ba su dawo gida ba

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262