Babban Kwamanda da Daruruwan Yan Ta’adda da Harin Amurka, Najeriya Ya Yi Ajali

Babban Kwamanda da Daruruwan Yan Ta’adda da Harin Amurka, Najeriya Ya Yi Ajali

  • Hedikwatar tsaron Najeriya ta yi karin haske kan harin Amurka da hadin guiwar Najeriya wanda ya yi ajalin yan ta'adda
  • Rundunar sojoji ta bayyana cewa hare-haren haɗin guiwa da Amurka suka kai sun kashe mayaƙan ISIS 175 a Arewa maso Gabas
  • Hukumar tsaron ta tabbatar da cewa hare-haren sun lalata sansanonin ’yan ta’adda tare da karya hanyoyin kuɗi da kayan aikinsu a yankin

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Abuja - Hedikwatar tsaron Najeriya ta bayyana yadda harin Amurka da hadin guiwar Najeriya ya yi ajalin babban kwamanda a Arewa maso Gabas.

Rundunar tsaro ta ce hare-haren haɗin guiwa da rundunar AFRICOM ta Amurka suka kai sun kashe mayaƙan ISIS 175.

Harin Amurka da Najeriya ya hallaka yan ta'adda
Shugaba Bola Tinubu da takwaransa na Amurka, Donald Trump. Hoto: Bayo Onanuga, Donald J Trump.
Source: Getty Images

Hakan na cikin wata sanarwa ta rundunar ta wallafa a shafinta na X a yau Talata 19 ga watan Mayun shekarar 2026.

Kara karanta wannan

Duk da ƙaryata Amurka, an tabbatar da hannun Trump a hallaka jagoran ISIS a Najeriya

A cikin sanarwar da Daraktan yaɗa bayanan tsaro, Birgediya Janar Samaila Uba ya fitar, an bayyana harin a matsayin babban nasara.

Harin Amurka, Najeriya ya hallaka yan ta'adda

Sanarwar ta ce hare-haren da aka fara kwanaki kaɗan da suka gabata sun lalata shingayen ’yan ta’adda da ma’ajiyar makamai da kayayyakin yaƙi.

Sojojin sun kuma ce hare-haren sun lalata cibiyoyin sufuri, kayan aikin soja da hanyoyin kuɗaɗen da ke tallafa ayyukan ISIS a yankin.

Hedikwatar tsaron ta ce ɗaya daga cikin waɗanda aka kashe shi ne Abu-Bilal al-Minuki, wanda aka bayyana a matsayin babban ɗan ISIS a duniya.

Sojoji sun ce al-Minuki yana taka muhimmiyar rawa wajen shirya hare-hare, samar da kuɗi, ɗaukar mayaƙa da tsara ayyukan ta’addanci a duniya.

An hallaka yan ta'addan ISIS 175 a Najeriya
Ministan tsaron Najeriya, Christopher Musa. Hoto: HQ Nigerian Army.
Source: Facebook

Yadda harin ya raunana ayyukan kungiyar ISIS

Sanarwar ta ƙara da cewa mutuwarsa ta girgiza tsarin jagoranci da ayyukan ISIS tare da raunana shirye-shiryen hare-haren ƙungiyar.

Hedikwatar ta kuma bayyana wasu jagororin ta’addanci da aka kashe da suka haɗa da Abd-al Wahhab da Abu Musa al-Mangawi da sauransu.

Kara karanta wannan

Trump ya nanata barazanar kawar da Iran daga doron kasa, ya fadi dalili

An kuma kashe Abu al-Muthanna al-Muhajir, wanda ake zargi da kula da yaɗa bidiyoyi da harkokin yaɗa labaran ISIS a yankin.

Sojoji sun ce zuwa ranar 19 ga Mayun 2026, bayanai sun nuna cewa mayaƙan ISIS 175 ne aka kashe a hare-haren haɗin gwiwar.

Hedikwatar tsaron ta bayyana cewa rundunar sojin Najeriya za ta ci gaba da matsa wa ƙungiyoyin ta’addanci lamba a sassan ƙasar nan.

Ta kuma tabbatar wa ’yan Najeriya cewa haɗin gwiwa da rundunar AFRICOM zai ci gaba domin kare tsaron ƙasa da zaman lafiyar yanki.

Al-Minuki: Rundunar ta saba da bayanan Amurka

An ji cewa hedikwatar tsaro ta yi karin haske game da rahotanni kan kisan hatsabibin dan ta'adda, Abu Bilal Al-Minuki da aka yi.

Rundunar ta bayyana gaskiya kan rawar kasar Amurka da ta ke ikirarin ta hannunta aka kashe kashe shugaban ISIS Abu Bilal Al-Minuki.

Janar Michael Onoja ya ce Amurka ta bayar da tallafin bayanan sirri, sa ido da bincike kawai, ba tare da tura sojojinta ba.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.